Rundunar ‘Yansandan Babban Birnin Tarayya, Abuja, ta kama wata mata mai suna Beauty Monday bisa zargin kwara wa maƙwabciyarta ruwan zafi a unguwar Lugbe.
Kakakin ’yansandan, Josephine Adeh, ta ce lamarin ya faru ne ranar 4 ga watan Satumba bayan matan biyu sun samu saɓani kan amfani da wani fili da suke tarayya a cikin gidansu.
A cewar ’yansanda, wadda aka zuba wa ruwan zafin, Gift Amos, ta sauke tukunyar ruwan zafin da ke kan murhu.
Ana zargin Beauty da fusata, lamarin da ya sanya ta ɗauki tukunyar ta zuba ruwan a bayan Amos, lamarin da ya jawo mata munanan raunuka.
A yanzu haka ana kula da Gift Amos a asibit.
An gurfanar da Beauty Monday a gaban kotu, sannan aka tura ta gidan gyaran hali na Suleja.
An ɗage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 16 ga watan Satumba.
Kwamishinan ’yansandan Abuja, Ahmed Muhammed Sanusi, ya shawarci jama’a da su riƙa warware rikice-rikice cikin lumana tare da guje wa tashin hankali.













