• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar Kuɗin Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki – Masana

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Tattalin Arziki
0
Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar Kuɗin Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki – Masana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana harkokin kudi da na tattalin arziki sun bayyana wa Shugaban kasa Bola Tinubu cewa karuwar kaso 3.19 na kudin shigar Nijeriya a zango na biyu na 2024 ya gaza fito da hakikanin halin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar kiddiga ta Nijeriya (NBS) ta sanar a ranar Litinin cewa kudin shigan Nijeriya ya karu da kaso 3.19 cikin 100 a zango na biyu na shekarar 2024, wanda ya dara da kaso 2.98 cikin 100 a zangon farko.

  • Kamfanin Abinci Na BUA Ya Samu Ribar Naira Biliyan 130 A Wata Shida Na 2024
  • Yawan Ribar Da Masana’Antu Masu Matsakaicin Kudin Shiga Suka Samu Ya Karu Da Kashi 3.6% A Farkon Watanni 7 Na Bana

A cewar rahoton NBS, bangaren kamfanoni da ayyuka sun ba da gagarumin gudunmawa wajen ci gaban kudin shigan a zango na biyun.

Bangaren ayyukan yau da kullum ya ba da kaso 58.76 na kudaden shiga, inda bangarorin da ba na mai ba suka kawo kaso 94.30, yayin da kuma bangaren mai ya kawo kaso 5.70 a zango na biyun.

Duk da wannan ci gaban da kudin shigan kasan ya samu, masana tattalin arziki sun yi tambayar mene ne ya sanya har yanzu talakawan Nijeriya ba su ga tasirin karin da aka samu ba.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

Bugu da kari, farashin kayayyaki na nan a kan tsadarsu duk da tsare-tsaren da Tinubu ya bijiro da su.

Wani masani kan tattalin arziki, Farfesa Segun Ajibola, tsohon shugaban kungiyar kwararru a bangaren banki, ya ce, ci gaban bai taba rayuwar talakawa ba ko kawo sauyi daga halin da suke ciki.

Ya nemi gwamnati da ta bullo da hanyoyin da suka dace da talaka zai samu sauki da ganin tasirin ci gaban da ake samu na kai tsaye.

A cewarsa, ci gaban ya kamata ne ya shiga cikin abubuwan da suke na bukatun jama’a na farko-farko wato irin kayan abinci kafin a je ga manyan bangarori na ayyukan yau da gobe, wanda in aka samu hakan talaka zai shaida.

Shi ma masanin hada-hadar kudade, Gbolade Idakolo, ya ce, karuwar kudin shigan bai janyo sauyi kan lamarin tattalin arziki daga tushe a wajen talaka ba.

Don haka ne ya ce a yi la’akari da hakikanin halin da ake ciki ta yadda za a nemi tunkarar abubuwan da suke akwai domin samun sauyi mai ma’ana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KudiMoneyTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Dauda Ya Ziyarci Yankunan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Gummi

Next Post

Zaben Kananan Hukumomin Kano: ‘Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

Related

Dangote
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

1 week ago
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote
Tattalin Arziki

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

1 week ago
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
Tattalin Arziki

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

2 weeks ago
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta
Tattalin Arziki

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

2 weeks ago
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

3 weeks ago
NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku
Tattalin Arziki

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

3 weeks ago
Next Post
Zaben Kananan Hukumomin Kano: ‘Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

Zaben Kananan Hukumomin Kano: 'Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.