• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

by Abubakar Abba
9 months ago
in Tattalin Arziki
0
Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wake na daya daga cikin amfanin gonar da aka dakatar da shigar da da shi daga Nijeriya zuwa Tarayyar Turai.

Wasu kwararru sun yi gargadin cewa, akwai yiwuwar farashin Wake ba zai sauka ba a wannan kasa da muke ciki.

  • Kakar Da Ta Fi Dacewa Da Noman Wake A Nijeriya
  • Nazari Kan Lokacin Da Ya Fi Dacewa A Shuka Wake A Nijeriya

Kazalika, Cibiyar Kula da Fitar da Kayayyaki Kasashen Waje ta Kasa (NEPC) ta sanar da cewa, Nijeriya na noma Wake mai dimbin yawa; wanda ya kai kimanin kashi 58 cikin 100 na yawan wanda ake bukata a duniya.

Sai dai, wasu matsaloli da suka hada da ayyukan ‘yan bindigar daji, yawan rikice-rikice a tsakanin manoma da makiyaya da sauran makamantansu, an danganta su a matsayin manyan kalubalen da ke jawo rashin noman Waken da dama a Nijeriya.

Bugu da kari, akwai kuma kalubalen rashin kayan aiki; da suka hada da samar da wurin adana shi da rashin yin amfani da dabarun zamani, wanda hakan ya jawo rashin samar da wadatuwar sa a fadin wannan kasa.

Labarai Masu Nasaba

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Shugaban Kungiyar Manoma na Kasar, reshen Jihar Kano (AFAN); Alhaji Abdulrasheed Magaji Rimin Gado ya sanar da cewa, sauyin yanayi da kuma matsalar rashin tsaro, sun yi matukar taka muhimmiyar rawa wajen kawo raguwar noman wannan Wake.

An ruwaito cewa, Jamhuriyar Nijar; na tura kimanin kashi 45 cikin 100 na Waken da take nomawa zuwa wasu jihohin Arewacin Nijeriya, inda ake hada-hadar kasuwacninsa ta hanyar musayar Naira da kuma takardar kudin CFA, wanda hakan ko kadan baya taimakawa wannan fanni.

Magaji ya ci gaba da cewa, manyan dillalansa ba sa iya shigo da shi cikin wannan kasa, sakamakon matsalar samun kudaden musaya da ba sa iya samu.

Ya kara da cewa, lamuran na ci gaba da kara munana; musamman idan aka yi la’akari da wani rahoto da ya riske mu da ke nuna cewa, Jamhuriyar ta Nijar ta dakatar da fitar da amfanin gona daga kasar zuwa wasu kasashe, ciki har da Nijeriya.

A cewarsa, hakan ba zai bari farashinsa da sauran kayan amfanin gona su ragu ba.

Ya sanar da cewa, akwai matukatar bukatar a bai wa noman rani muhimmanci, musamman don cike gibin da aka samu a noman damina na bana.

Kazalika, ya sanar da cewa, ya zama wajibi gwamnati ta kayyade farashi, musamman a kan Wake domin samar da wadatuwarsa; cikin kuma farashi mai sauki.

Shi ma, wani babban dila a Kasuwar Hatsi ta kasa da kasa a Kasuwar Dawanau ta Jihar Kano, Alhaji Musa Gawuna ya bayyana cewa; ba a noman Wake da yawa, duk kuwa da matukar bukatar da ake da shi.

A cewarsa, wasu manoman; musamman na Waken, na kauracewa gonakinsu, saboda yawan samun rikice-rikicen manoma da makiyaya, wanda hakan ya dakatar da manoman daga yin nomansa kamar yadda aka yi tsammani.

Rahotannin sun ce, mahukuntan soji na kasar Nijar, sun dakatar da fitar da Shinkafa da sauran amfanin gona zuwa sauran kasashen duniya.

Sun dauki wannan matakin ne, biyo bayan barazanar da kungiyar ECOWAS ta yi wa mahukuntan kasar na cewa, tilas ne su mayar da kasar kan turbar mulkin dimokradiyya; bayan juyin mulkin da suka yi a kasar a shekarar da ta gabata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Wake
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

Next Post

Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

Related

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

18 hours ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

19 hours ago
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

20 hours ago
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

1 week ago
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
Tattalin Arziki

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

1 week ago
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
Tattalin Arziki

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

2 weeks ago
Next Post
Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.