ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

by Abubakar Abba
10 months ago
Jirage

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama ya yi tir da dabtarin kudin yarjejeniyar sayar da hannun sayar da hannun jarin daukacin Tashoshin Jiragen Sama na kasar.

Sun sanar da cewa, akwai rashin bin ka’ida da masu ruwa da tsaki a fannin suka yi kan wannan batun.

  • Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
  • Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Ma’aiktan sun bayyana, yarjejeniyar ta sabawa ka’ida kuma ‘ya’yan kungiyar, ba su da wata masaniya kan batun.

ADVERTISEMENT

Kazalika, sun soki Gwamnatin Tarayya kan zagaye Ma’aikatan da kuma sauran kungiyoyin na da ke tafiyar da Sufurin Jiragen Sama tare da kuma yin watsi da bukatun Ma’aikatan.

A cewar, Ma’aiktan bisa ka’ida kamata ya yi Gwamnatin Tarayya ta wallafa batun na yarjejeniyar a manyan Jaridun kasar kasar a matsayin talla har zuwa tsawon watanni shida yadda duk wani mai bukata shiga cikin yarjejeniyar zai samu damar shiga cikin sahun masu nema

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

A farkon wannan shekarar da ta gabata, Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, a wani taro ya bai wa kungiyoyin na Sufurin Jiragen Sama tabbacin cewa, Gwamnatin Tarayya za ta tabbatar da bi ka’ida wajen sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman kasa.

Keyamo ya kuma bai wa shugabannin kungiyoyin tabacin cewa, suma a sanya kan batun na yarjejeniyar ta sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman.

Kazalika, ba su tabbacin cewa, zai umarci hadiminsa domin ya ci gaba da sanar da shugabannin kungiyoyin kan abinda ke tafiya game da yarjejeniyar.

Sai dai, a jawabin da shuwagabbin kungiyar da kuma na ma’aikatan suka gabatar a wani babban taronsu a shalakwar Tashar Jiragen Sama da ke a jihar Legas, sun soki Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, bisa zagaye shugabannin kungiyoyin kan batun na jarjejeniyar.

A jawabinsa shugaban kungiyar ma’aikatan zirga-zirga ta jiragen sama na kasa NUATE Kwamarade Ben Nnabue ya yi kira da sake sabon lale kan batun na yarjeniyar musamman domin a bai wa sauran masu ra’ayin shiga cikin yarjejeniyar.

“Ya kamata a sake faro yarjejeniyar tun daga farkonta, domin a bai wa sauran ‘yan Nijeriya damar shiga cikin yarjejeniyar,”Inji Shugaban.

Nnabue ya ci gaba da cewa, a matsayinsu na shuwagabannin kungiyoyin sam ba su da wata masaniya game da wannan yarjejiniyar da da Gwamnatin ta kulla.

Ya kara da cewa, hatta shuwagabannin kungiyoyin kwadago ba a sanar da su, game da yarjejiniyar ba, amma sai kawai muka ji, Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, sanar da cewa, Majalisar Zartwar kasar ta amince da wannan yarjejeniyar, musamman ta Tashar Jirgin Sama na jihar Enugu.

“Muna son mu sanar da duniya cewa, dole kafin a gudanar da duk wata yarjejniya a fara tattaunawa da shuwagabbin kungiyoyin kwadago tukunna, ” A cewar Kwamarade Ben.

Ya sanar da cewa, hanyoyin da ake bi na gudanar da wannan yarjejeniyar, cike take da kura-kurai domin ba mu da wata masaniya ko an bayar da talla ga manyan Jaridun kasar nan kan batun na yarjeniyar.

“Tashoshin Jiragen Sama na kasar nan, mallakin ‘yan Nijeriya, a saboda haka ba za ta sabu kawai a cikin dare daya mu ji an yanke shawarar cewa, akwai wasu ‘yan lele da ake so su kadai a yi yarjejeniyar da sub a, domin kamata ya yi ba bar abin a bude domin suma ‘yan kasar, su gyada ta su sa’ar, a saboda haka, muna bukatar a soke wannan yarjejniyar har sai idan an bi ka’idar da ta dace, “ Inji shugaban.

Shi ma a na sa bangaren shugaban kungiyar kwarru ta ANAP Kwamarade Alale Adedayo, ya yi tir da hanyoyin da Ministan ya bi domin yin wannan yarjejeniyar ba tare da janyo shugabannin kungoyoyin ba kamar yadda ya yi masu alkwari a baya.

Kwamarade Adedayo ya bukaci da sake sabon lale kan batun wannan yarjejeniyar, musamman domin a tabbatar da an bi ka’aida da kuma yin gaskiya.

Jirage
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.