Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, ta ce akwai shaidu na hakika game da ayyukan ta’adda da dakarun Japan suka aikata, yayin yakin duniya na biyu, an kuma killace wadannan shaidu cikin kundin shari’un da aka gudanar a birnin Tokyo.Da yake tsokaci dangane da wannan batu, kakakin ma’aikatar Lin Jian, ya ce a bana ake cika shekaru 80, da bude shari’un da suka gudana a birnin Tokyo.
Kuma a baya-bayan nan kasar Sin ta wallafa fassarar cikakkun bayanai na kotun kasa da kasa, ta hukunta jami’an soji na bangaren gabas mai nisa, wanda ya zamo muhimmin kundin bayanai a tarihin shari’un, kuma wanda ya tattara daukacin bayanai na shari’un da aka kwashe sama da shekaru biyu ana gudanarwa.
Lin Jian, wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, ya ce duk da shudewar shekaru 80, wasu masu tsattsauran ra’ayi daga bangaren Japan, sun gaza yin karatun ta nutsu game da tarihi, maimakon hakan sun ci gaba da kokarin kare mummunan ayyukan murdiya, da ingiza matakin jirkita mahangar tarihi tsakanin al’ummun kasar ta Japan.
Daga nan sai jami’in ya ce jama’a masu kaunar zaman lafiya a dukkanin sassan duniya, ba za su bari wani yunkuri ya sauya sakamakon shari’a dangane da yakin danniya ba, kana za su ci gaba da yin adawa da manufar Japan ta farfado da bayyana karfin soji. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post