Shugabannin tashar jiragen ruwa, ta Onne da ke Fatakwal Jihar Ribas sun karrama wadanda suka yi ritaya daga aikin duk da yake ana ta mika godiya zuwa ga Shugaban Hukumar jiragen ruwa ta kasa, Dakta Abubakr Dantsoho saboda yadda yake kulawa da su sosai.
An yi bikin ne ranar Laraba, 22 ga Afrilu, 2026, a ofishin hukumar da ke the Onne Fatakwal babban birnin Jihar,bikin wanda za a dade ana kulawa da shi ne, domin za a rika tunawa da rayuwa irin ta neman wa ma’aikata hakkinsu, abu ma mafi muhimmanci shi ne nuna kauna da soyayya kamar yadda aka nunawa wadanda suka yi ritayar da Shugabannin hukumar suka yi ma su.
Da yake magana da manema labarai a wurin bikin, Manajan tashar,Onne, Mista Abdulrahmon Hussain sya bayyana dalilin bikin ko taron shi ne domin a nuna an ji dadin abinda wadanda suka yi ritayar suka yi, domin kuwa sune suka dora tubulin wurin, buga da kari kuma sune suka reni yawancin ma’aikatan a Onne.
Ga maganar da ya yi: “Abinda Shugabannin tashar jirgin ruwa ta Onne suke ke yi yau shi ne domin su nuna cewa sun ji dadin abinda ma’aikatan da suka yi ritaya suka yi.”
Da yake kara yin bayani, cewa ya yi “muna da sane cewar wannan wurin da muka kasance a yau wadanda suka yi ritayar ne suka kafa tubalin shi.”
“Lokacin da suke aiki, su ne suka reni kananan ma’aikatan mu, sun kuma bada matukar gudunmawa wajen girma da ci gaban wannan tashar Jirgin ruwa.”
“Maganar gaskiya, kun san ana kiran shi da suna “Wuri ne kuma tasha ta iyali” mu kuma maganar gaskiya mun son mu nuna masu cewa har yanzu suna daga cikin mambobi na iyali duk kuwa da yake sun yi ritaya.”
Da yake magana game da zuwan wadanda suka yi ritaya, Manajan tashar jirgin ruwan ya kara yin bayani mai kamar haka”da ganin su ka san su ba gajiyayyu bane,suna da karfi, farin ciki da kuma koshin lafiya,Ina mika dukkan godiya ga Allah da suka kasance suna cikin koshin lafiya ,wannan zai zama suma Shugannnin wurin a gode ma Shugaban Hukumar, Dakta Abubakar Dantsoho da shi da ‘yan tawagarsa saboda irin kulawar da suke yi da wadanda suka yi ritaya.”
“Ina kira da su cewa duk yadda za su yi su yi kokari da ci gaba da ku kare jikinsu domin kasancewa cikin koshin lafiya ba tare da kara kibar da za ta zama matsala a gaba, kamar yadda Shugaban” tashar ruwa ta Onne ya fada.
Ya ci gaba da bayani “Bikin wannan rana ta yau shi ne na farko da aka taba yi, sai dai mun yi alkawari za mu wanda za ayi nan gaba zai zarce na yau.”
“Bayan multibitamins da sauran magunguna da muka ba su, kamar yadda na ke gani babban abinda ya fi shi ne nuna kauna da kulawa da Shugabannin wurin suka yi, shekara mai zuwa abinda za ayi zai zarce wannan kamar yadda su Shugabannin suke da niyya yin hakan” kamar dai yadda ya kara jaddadawa.
Shi ma a jawabin sa, babban jami’in lafiya,(CMO) na tashar jirgin ruwa ta Onne Dokta. Bashir Kangiwa ya jinjinawa su Shugabannin saboda tsarin da suka bullo da shi wannan shi ne na farko da aka taba yi.















Discussion about this post