Mazauna ƙaramar hukumar Shinkafi a Jihar Zamfara sun yaba wa sojojin Operation Fansan Yamma bisa ci gaba da yaƙar ’yan bindiga a yankin.
Wani manomin shinkafa mai suna Ahmed Rufai ya ce mazauna yankin sun samu zaman lafiya cikin makonni biyu da suka gabata, sakamakon ayyukan sojojin.
Wani shugaban al’umma, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ayyukan sojojin sun raunana ƙarfin ’yan bindigar na gudanar da ayyukansu.
Sai dai ya ce masu kai wa ’yan bindiga bayanan sirri daga cikin al’umma har yanzu su ne babbar matsala.
Wani jami’in soja ya ce sojojin sun yi arangama da wasu da ake zargin ’yan bindiga ne a kan babura a ranar Talata yayin wani samame a Shinkafi.
Sojojin sun buɗe musu wuta, inda suka kashe ɗaya daga cikinsu, yayin da sauran suka tsere.
Sojojin sun kuma ƙwato wayoyi guda huɗu da kuɗi Naira 30,350 daga hannun wanda suka kashe.
Sojojin sun ce aikin na daga cikin matakan da ake ci gaba da ɗauka domin rage ayyukan ’yan bindiga da ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Yamma.













