Rundunar ’yansandan Nijeriya ta kama wata matashiya mai shekaru 27, Hafsat Abubakar, bisa zargin ƙirƙira da yaɗa wata takardar ƙarya cewa kamfanin OPay zai daina aiki a Nijeriya.
Kakakin rundunar, Anietie Iniedu, ya bayyana hakan ranar Laraba a Abuja.
Ya ce OPay ce ta kai wa ’yansanda ƙara a ranar 31 ga watan Agusta, inda ta buƙaci a binciki tare da gano mutanen da suka ƙirƙira da yaɗa takardar.
A cewar Iniedu, jami’an cibiyar yaƙi da laifukan Intanet sun yi amfani da hanyoyin binciken zamani wajen gano cewa an fara yaɗa takardar ne a shafin X da Hafsat Abubakar ke amfani da shi.
’Yansanda sun kama Hafsat a ranar 4 ga watan Satumba.
Ta kammala karatun Library and Information Science a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.
’Yansanda sun ce irin wannan labarin na iya jefa jama’a cikin fargaba, haddasa asarar kuɗi da kuma ɓata sunan kamfani.
OPay ya riga ta musanta labarin da aka yaɗa a kafafen sada zumunta cewa kamfanin zai daina aiki daga ranar 1 ga watan Satumba.
Kamfanin ya ce sanarwar ba gaskiya ba ce kuma OPay na ci gaba da aiki yadda ya kamata.
Ya kuma ce takardar tana da kura-kurai da dama, ciki har da tsohon tambarin kamfanin, kuskuren rubuta sunan OPay da kuma tsarin rubutu da bai yi kama da sanarwar kamfanin ba.
’Yansanda sun ce suna ci gaba da bincike a kan lamarin kuma duk wanda aka samu da hannu zai fuskanci hukunci a gaban kotu.













