Adadin mutanen da suka mutu sakamakon ɓarkewar cutar mashaƙo a Jihar Filato ya ƙaru zuwa 27, yayin da adadin waɗanda ake zargin sun kamu da cutar ya kai 303.
Likitan kula da cututtuka masu yaɗuwa na jihar, Dokta Maren Damulak ne, ya bayyana hakan a ranar Laraba a Jos.
Ya ce kashi 99 cikin 100 na waɗanda ake zargin sun kamu da cutar suna Jos ta Arewa
Damulak ya ce yawancin mutanen da cutar ta kama ba su yi allurar rigakafin cutar mashaƙo ba.
Ya kuma ce yara na daga cikin waɗanda cutar ta fi shafa, yayin da al’ummar Rikkos da ke Jos ta Arewa na daga cikin wuraren da cutar ta fi ƙamari.
A makon da ya gabata, gwamnatin jihar Filato ta bayar da umarnin rufe makarantun firamare da sakandare na gwamnati da masu zaman kansu, bayan gano waɗanda ake zargin sun kamu da cutar a Jos ta Arewa, Jos ta Kudu, Bassa da Wase.
Gwamnatin ta ce matakin na da nufin rage yaɗuwar cutar tsakanin ɗalibai da ma’aikatan makarantu, yayin da hukumomin lafiya ke sa ido da ɗaukar sauran matakan daƙile cutar.
Wasu daga cikin marasa lafiyar na samun kulawa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos (JUTH) da Asibitin Kwararru na Jihar Filato, inda aka tanadi wuraren killace waɗanda suka kamu da cutar.
Haka kuma, ƙaramar hukumar Jos ta Arewa ta ƙara samar da babura da sauran kayan aiki domin taimakawa wajen gano mutanen da suka yi hulɗa da masu cutar, sa ido da wayar da kan al’umma.
Gwamna Caleb Mutfwang ya bayar da umarnin gaggauta samar da magunguna da sauran kayan aikin lafiya a asibitoci domin taimakawa wajen shawo kan cutar.
A nasa ɓangaren, shugaban ƙaramar hukumar Jos ta Arewa, John Kyohroh Christopher, ya yi kira ga mazauna yankin da su kula da tsaftar jiki da muhalli domin rage yaɗuwar cutar.












