Ambaliyar ruwa ta tafi da wasu yara biyu ‘yan shekara 13 a Abuja da Jihar Abia bayan ruwan sama mai ƙarfi.
A Gwagwalada da ke Abuja, Alhassan Jamil, ɗalibin ƙaramar sakandare, ambaliyar ruwa ta tafi da shi a safiyar ranar Laraba yayin da yake kan hanyar zuwa makaranta tare da mahaifinsa a kan babur.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:30 na safe a kusa da wani gidan mai da ke hanyar Old Kutunku-Market.
An ce yaron ya faɗa cikin wata magudanar ruwa da ruwa ya cika ta maƙil yayin da suke ƙoƙarin ketare hanya.
Mahaifinsa ya yi ƙoƙarin ceto shi, amma ƙarfin ruwan ya yi awon gaba da yaron.
An samo masunta da wasu mazauna yankin domin nemo shi, amma har zuwa lokacin da haɗa wannan rahoto, ba a gano gawarsa ba.
A Umuahia ta Jihar Abia kuma, wata yarinya ‘yar shekara 13, Adekunle Emanuella Ige, ambaliyar ruwa ta rutsa da ita a yammacin ranar Litinin.
Rahotanni sun ce yarinyar ta faɗa cikin wata babbar magudanar ruwa yayin da take dawowa gida lokacin ruwan sama mai ƙarfi.
Ruwan ya shafe magudanar, lamarin da ya sa ba a iya bambance magudanar da hanyar da ake bi.
Mazauna yankin sun fara neman yarinyar har zuwa ranar Talata, amma ba a samu nasarar gano ta ba.
Mahaifiyarta ta roƙi mazauna yankin da hukumomin gwamnati da su taimaka wajen nemo ‘yarta.
Lamarin sun haifar da tashin hankali kan hatsarin ambaliyar ruwa, musamman a wuraren da magudanan ruwa ba su da zurfi.
A Abuja, hukumomi sun sha gargaɗin mazauna yankunan da ambaliyar ruwa ke yawan shafa da su ɗauki matakan kariya.
Rashin isassun magudanan ruwa, toshewar hanyoyi da gine-gine a kusa da hanyoyin ruwa na daga cikin abubuwan da ke ƙara haddasa ambaliyar.













