An bukaci maniyyata aikin hajjin bana daga Jihar Filato da su yi addu’o’in kawo karshen matsalar rashin tsaro da yanzu ake fama da shi a jihar.
Gwamnan Jihar Barista Caleb Mutfwang, ne ya yi wannan kira a lokacin da yake wa maniyyatan aikin hajjin bana jawabin bankwana a harabar hukumar jin dadin alhazai ta jihar da ke a kan titin Bauchi a cikin garin Jos.
Gwamnan wanda ya nuna damuwarsa bisa tsawon lokacin da rikice-rikicen jihar ya dauka, ya ce tun da aka fara irin wadanda nan fadace-fadacen waye ne ya semi ribar a jihar.
Haka nan kuma ya bukaci iyaye da su kara zaga damtse wajen tarbiyar ‘ya’yansu, ya danganta matsalar rashin tsaro da ake samu a jihar a bisa gurbacewar tarbiyar da ake samu tsakanin yara matasa a jihar.
Ya yaba wa namijin kokarin da kumar jin dadin alhazai take yi na kammala ayyukan shirye-shiryen aikin hajjin a cikin lokaci kuma ya tabbatar wa hukumar samun kyakkyawar kulawar gwamnati daga nan gida Nijeriya har zuwa kasar Saudi Arabiya.Shi ma a jawabinsa, Amirul Hajjin bana daga jihar kuma tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Honarabul Maje Idris Wase, ya yaba wa gwamnan jihar, Barista Cleb Mutfwang, bisa sama wa mahajatan jihar 1,134, inifom da ihramai kyauta don saukake masu aikin hajjin.
Ya roki mahajjatan da su taimaka wa jihar da addi’o’in Allah ya kawo zaman lafiya dawwamamme a jihar da kasar baki daya.















Discussion about this post