ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Bunkasa Yanki Na —Sarkin Tilden Fulani

by lawal Umar Tilde and Sulaiman
4 months ago
Tilde

Kwanakin da suka gabata ne mai martaba Lamidon Toro na farko Alhaji Umaru Adamu, ya yi bikin nadin Hakimai Biyar da suke a karkashin masarautarsa, wanda Sarkin Garin Tilden Fulani Alhaji Aliyu Muhammadu Tukur na daya daga cikinsu, Wakilinmu na Jos Lawal Umar ya samu ganawa da shi, ga dai yadda hirar ta su ta kasance.

 

Zan yi farin ciki, idan ka gabatar ma ni da kanka?

ADVERTISEMENT

Sunana, Alhaji Aliyu Muhammad Tukur, Sarkin Yamman Toro, Hakimin Kasar Tilden Fulani.

 

LABARAI MASU NASABA

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

Kana daya daga cikin hakimai Biyar, da Mai martaba, Lamidon Toro na daya (1), Alhaji Umar Adamu, ya rantsar a kwanakin da suka gabata don yin aiki tare da shi a fadarsa, ya kaji me kuma za kace?

Naji dadi, koda yake, an kara, daure ni da Sarka ne, don haka dole ne in tashi in yi tsayuwar daka wajen yin aiki tukuru in kuma yi adalci daidai gwargwado, don in sauke nauyin da aka dora mani, don in samu kubuta ranar gobe kiyama. Idan na yi gaskiya shi ne hakan zai bani tsira da ga wadansu tambayoyi da za ayi mani a kabari, ina addu’a Allah S W T ya taimaka mani mini in sauke wannan nauyi da aka dora mani cikin nasara.

 

Ga shi ka gaji matsaloli masu yawa kama dada wadda ta shafi rashin tsaro, da kuma rashin abubuwan da za su inganta rayuwar al’umma, kamar rashin ingantccen ruwan sha, ta yaya za ka iya fuskantar lamarin?

Zan fara da matsalar rashin tsaro, domin ita ce tafi tayar da hankalin jama’a, ba nan yanki na kawai ba, Kusan dukkan kasa baki daya, maganar rashin tsaro ita ce tafi tayarwa mutane hankali, zan kara yin kokari in ga ‘yan bangarmu sun kara hada kai da jami’an tsaro da suka hada da sojoji, da ‘yansanda da aka turo su aiki, a nan yankin domin su rika aiki tare dare da rana, wajen yin yaki da miyagun mutane masu kawo barazana da rayuwar al’umma.

Zan kuma bukaci babban jami’in ‘yansanda, (DPO) na wannan gari da shugabannin addini da na al’ummomi, da na ‘yansiyasa, da sauran kungiyoyi, da ke zaune, a wannan yanki da su kara badai hadin kai wajen cimma wannan burin. Za kuma mu toshe duk wata kofa da muke ganin mugayen mutane za su iya yin amfani da ita domin su aikata barna, masu unguwanni kuma su tabbatar da sun tantance bako kafin su bari ya sayi gida ko Folotin, da zai gina gida ko kuma gonar da zai yi noma.

 

Duk da yake a baya an taba baka wannan mukami amma daga baya aka soke sai kuma ga shi wannan gwamwnatin karkashin jagorancin Gwamnan Jihar Bauchi Sanata Bala Mohammed, ya sake maida maka da mukamin ya kaji maye za kace?

Na ji dadi ba abinda zan ce sai dai, in kara yi wa Allah godiya da ya kawo mu zuwa wannan lokaci ga gwamnan mu Sanata Bala Mohammed ina mai godiya kwarai da gaske, domin da a baya tsohon Gwamna Isa Yuguda, ya nada mu wadannan mukamai na Hakimai, amma daga baya Gwamnan Muhammed Abubakar, ya zo ya sauke mu, ga shi yanzu wannan gwamna mai adalci, ya sake maido mana da mukaman har ma ya kara kirkiro da sabbin masarautu da kuma daga darajar wadansu, ba abinda za nce wa gwamna sai dai in kara yin masa addu’a, Allah ya kara taimaka masa akan kokarin da yake na kawo ci gaban al’umna da na tattalin arzikin jiha, ya kuma kara ba shi lafiya da basiràr ta tafiyar da ayyukan sa cikin nasara.

 

Ka san cewa zaka yi aiki tare da maimartaba Lamidon Toro,na farko Alhaji Umar Adamu, wane tabbaci za ka yi masa na samun goyon bayan al’ummar masarautarka?

Mai Martaba Lamidon Toro, Alhaji Umar Adamu, ina kara tabbatar masa samun goyon mutanen wannan gunduma dari bisa dari, akan duk wani aiki da zai iya tasowa don ci gaban mutanen wannan karamar hukuma da kuma jihar Bauchi baki daya.

 

Kasancewa kasar ka ta yi iyaka da jihar Filato, da rikice- rikicen siyasa da na kabilanci, yaki ci yaki cinyewa wane kokari za ka yi wajen kawo hadin kai a tsakanin al’ummomin da ke zaune nan yankin kasar ka da na jihar Filato?

Wannan na daya daga cikin abinda ya fi damuna, domin wannan rikici ya dauki lokaci mai tsawo tun a shekarar 2001, da aka fara rikici a tsakanin al’ummomin jihar Filato, da da su ke zaune lami lafiya da junansu amma ga shi har yanzu ba’ a daina fada ba, ga shi har an kai shekara Ashirin da biyar ke nan wannan ai abin damuwa ne matuka, ina fata gwamnati da masu ruwa da tsaki akan harkar kawo zaman lafiya a Filato za su dauki sabbin matakai don kawo karshen wannan rikicin.

Ya ce, rikicin ya haddasa kwararowar baki masu dimbin yawa zuwa yankin gundumar sa kuma ya bukaci gwamnatin jihar Bauchi da gwamnatin tarayya, da su taimakawa al’ummomin da su ke zaune, a yankin da abubuwan more rayuwar jama’a.

Bugu da kari saboda karuwar al’umma mutanen yankin na fuskantar karancin ababen more rayuwa kamar tsaftatatcen ruwan sha, rashin ingantancen hasken-wutar lantarki, rashin ingantattun hanyoyin-mota daga karkara zuwa birane, karancin azuzuwa na makarantun gwamnati, da kuma karancin jami’an tsaro da dai sauransu.

Kungiyoyin al’umma da na addinai, da na yan-siyasa, da mutane sai zuwa suke yi Fadar Sarkin suke yi don nuna mubaya’arsu da taya shi murna da addu’o’in fatan alkhairi su ke ta yi.

 

Mun gode

Nima na gode

Tilde
lawal Umar Tilde
+ posts Bio
  • lawal Umar Tilde
    https://hausa.leadership.ng/author/lawal-umar-tilde/
    An Bukaci Maniyyata Daga Filato Su Yi Addu’o’in Kawo Karshen Rashin Tsaro A Jihar
  • lawal Umar Tilde
    https://hausa.leadership.ng/author/lawal-umar-tilde/
    Kamfanonin Taki Na Gida Za Su Iya Taimaka Wa Gwamnati Wajen Tallafa Wa Manoma
  • lawal Umar Tilde
    https://hausa.leadership.ng/author/lawal-umar-tilde/
    Kishin Ƙasa Da Tsoron Allah Ne Mafita Daga Matsin Tattalin Arziƙin Ƙasar Nan – Malam Usman
  • lawal Umar Tilde
    https://hausa.leadership.ng/author/lawal-umar-tilde/
    An Nemi Gwamna Mutfwang Ya Yi Takatsantsan Da ‘Yan Barandar Siyasa
Tilde
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattaunawa

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

July 11, 2026
Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu
Tattaunawa

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

April 10, 2026
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Tattaunawa

Dalilin Da Ya Sa PDP Ke Cikin Rikici, Za Ta Dawo Da Karfin Ta —Saraki

April 4, 2026
Next Post
Amotekun Ta Kuɓutar Da Ma’aikatan Lafiya 3 Da Wasu Biyu Daga Hannun Masu Satar Mutane

Amotekun Ta Kuɓutar Da Ma’aikatan Lafiya 3 Da Wasu Biyu Daga Hannun Masu Satar Mutane

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.