A yau Alhamis ne aka bude dandalin kasa da kasa game da tsarin jagorancin hakkin dan Adam na shekarar 2026 a birnin Beijing, kuma memban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana shugaban sashen wayar da kan jama’a ta kwamitin kolin JKS Li Shulei, ya halarcin bikin bude dandalin tare da gabatar da jawabi.
An bude dandalin na yini biyu ne da taron gama gari, wanda ya hallara sama da baki 400, daga cikin kasar Sin da kasashen ketare sama da 100, da kuma wakilai daga MDD, da wasu hukumomin kasa da kasa da na shiyyoyi.
Taron ya mayar da hankali ga jigon ingiza kare hakkin bil’adama ta hanyar samar da ci gaba, yana kuma gudana a gabar da ake cika shekaru 40 da amincewa da yarjejeniyar MDD ta bunkasa kare hakkin bil’adama.
Bugu da kari, ana sa ran mahalarta taron za su yi musayar ra’ayoyi game da batutuwan da suka shafi tsarin jagorancin hakkin bil’adama, da lalubo hanyoyin kare hakkokin bil’adama ta hanyar samar da ci gaba, da hadin gwiwar kasa da kasa da raba nasarorin ci gaba. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post