Gwamnatin Mexico ta umarci rufe makarantu a birnin Mexico tare da bai wa wasu ma’aikata damar yin aiki daga gida saboda fara gasar cin kofin duniya ta 2026.
Shugabar ƙasar, Claudia Sheinbaum, ta ce an ɗauki matakin ne domin rage cunkoson ababen hawa da kuma tabbatar da tsaro yayin wasan buɗe gasar da za a buga tsakanin Mexico da Afirka ta Kudu a filin wasa na Azteca.
A cewarta, ɗaliban makarantu na gwamnati da masu zaman kansu a babban birnin ba za su je makaranta ba a ranar Alhamis.
Haka kuma, ma’aikatan gwamnatin tarayya za su yi aiki daga gida, yayin da aka buƙaci kamfanoni masu zaman kansu su yi irin wannan tsari ga ma’aikatan da ba dole sai sun kasance a ofis ba.
Sai dai matakin bai shafi ma’aikatan lafiya, jami’an tsaro, ma’aikatan muhimman ayyukan gwamnati da kuma waɗanda ke da alaƙa kai-tsaye da gudanar da gasar ba.
Ana sa ran dubban magoya baya, jami’ai da masu yawon buɗe ido za su hallara a birnin Mexico domin kallon buɗe gasar.
Hukumomi na fatan cewa rufe makarantu na ɗan lokaci da kuma aiki daga gida zai taimaka wajen rage cunkoso da tabbatar da nasarar fara gasar cikin kwanciyar hankali.














Discussion about this post