Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ta kashe sama da Naira biliyan 928 wajen aiwatar da ayyukan ci gaba 1,508 a ƙananan hukumomi 44 na jihar tun bayan hawan Gwamna Abba Kabir Yusuf kan mulki. A cewar gwamnati, an kammala ayyuka 799, yayin da 709 ke ci gaba da gudana a matakai daban-daban.
Kwamishinan Ma’aikatar Saye da Kwangiloli ta Jiha, da Bibiyar Ayyuka da Tantance Su, Kwamared Nura Ma’aji Sumaila, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai kan ayyukan ci gaba da gwamnatin jihar ke aiwatarwa. Ya ce ayyukan sun shafi muhimman fannoni da suka haɗa da gina da gyaran hanyoyi, da inganta birane, da sufuri, da ilimi, da lafiya, da samar da ruwan sha, da tsaro da sauran ayyukan jama’a. Ya kuma bayyana cewa adadin bai haɗa da ayyukan mazabu 619 da ‘yan majalisar dokokin jihar ke aiwatarwa a faɗin ƙananan hukumomin Kano ba.
Sumaila ya ce gwamnatin ta bayar da kwangilolin da darajarsu ta kai kusan Naira biliyan 169 domin ayyukan inganta birnin Kano, ciki har da gyaran hanyoyi, gina magudanan ruwa da sauran ayyukan more rayuwa. Haka kuma, gwamnati na gina hanyoyi masu tsawon kilomita biyar a ƙananan hukumomi 38 ƙarƙashin kwangilolin da suka haura Naira biliyan 118, domin inganta zirga-zirga da bunƙasa tattalin arziƙin yankunan karkara.
Ya ƙara da cewa gwamnatin ta amince da kwangilolin da suka haura Naira biliyan 6.8 domin gina ofisoshin rundunar Neighbourhood Watch a ƙananan hukumomi 36, da nufin ƙarfafa tsaron al’umma. A cewarsa, ayyukan raya karkara da suka shafi ilimi, lafiya da sauran muhimman abubuwan more rayuwa a faɗin jihar sun kai sama da Naira biliyan 397, yayin da wasu ayyukan da ke gudana suka zarce Naira biliyan 255.
Ya tabbatar da cewa ma’aikatar za ta ci gaba da tabbatar da gaskiya, riƙon amana da ingancin ayyuka ta hanyar sa ido mai tsauri domin tabbatar da an yi amfani da kuɗaɗen jama’a yadda ya kamata.













