ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ta kashe sama da Naira biliyan 928 wajen aiwatar da ayyukan ci gaba 1,508 a ƙananan hukumomi 44 na jihar tun bayan hawan Gwamna Abba Kabir Yusuf kan mulki. A cewar gwamnati, an kammala ayyuka 799, yayin da 709 ke ci gaba da gudana a matakai daban-daban.

Kwamishinan Ma’aikatar Saye da Kwangiloli ta Jiha, da Bibiyar Ayyuka da Tantance Su, Kwamared Nura Ma’aji Sumaila, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai kan ayyukan ci gaba da gwamnatin jihar ke aiwatarwa. Ya ce ayyukan sun shafi muhimman fannoni da suka haɗa da gina da gyaran hanyoyi, da inganta birane, da sufuri, da ilimi, da lafiya, da samar da ruwan sha, da tsaro da sauran ayyukan jama’a. Ya kuma bayyana cewa adadin bai haɗa da ayyukan mazabu 619 da ‘yan majalisar dokokin jihar ke aiwatarwa a faɗin ƙananan hukumomin Kano ba.

Sumaila ya ce gwamnatin ta bayar da kwangilolin da darajarsu ta kai kusan Naira biliyan 169 domin ayyukan inganta birnin Kano, ciki har da gyaran hanyoyi, gina magudanan ruwa da sauran ayyukan more rayuwa. Haka kuma, gwamnati na gina hanyoyi masu tsawon kilomita biyar a ƙananan hukumomi 38 ƙarƙashin kwangilolin da suka haura Naira biliyan 118, domin inganta zirga-zirga da bunƙasa tattalin arziƙin yankunan karkara.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa gwamnatin ta amince da kwangilolin da suka haura Naira biliyan 6.8 domin gina ofisoshin rundunar Neighbourhood Watch a ƙananan hukumomi 36, da nufin ƙarfafa tsaron al’umma. A cewarsa, ayyukan raya karkara da suka shafi ilimi, lafiya da sauran muhimman abubuwan more rayuwa a faɗin jihar sun kai sama da Naira biliyan 397, yayin da wasu ayyukan da ke gudana suka zarce Naira biliyan 255.

Ya tabbatar da cewa ma’aikatar za ta ci gaba da tabbatar da gaskiya, riƙon amana da ingancin ayyuka ta hanyar sa ido mai tsauri domin tabbatar da an yi amfani da kuɗaɗen jama’a yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe
  • Abubakar Sulaiman
    Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu
  • Abubakar Sulaiman
    Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

MASU ALAKA

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

LABARAI MASU NASABA

Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.