Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, sun sake tayar da tsohuwar taƙaddamar su ta siyasa, inda suka yi musayar zarge-zarge kan wani zargin shirin tsige Obasanjo daga mulki da kuma batun neman wa’adi na uku da ya taɓa haddasa saɓani a tsakaninsu.
Obasanjo ya yi zargin cewa Atiku ya bai wa marigayi tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Umar Na’Abba, kuɗi har Naira miliyan 5 domin ya fara shirin tsige shi daga kujerar shugaban ƙasa a wa’adinsa na farko. Ya ce Atiku ya gana da Na’Abba a Fadar Shugaban Ƙasa tare da jan ra’ayinsa don ya fara tsarin tsigewar, yana mai cewa ya samu bayani ne daga tsohon Shugaban Ma’aikatansa wanda ya bayyana a matsayin ƙwararren jami’in leƙen asiri.
Sai dai a martaninsa, Atiku, ta bakin mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya musanta zargin baki ɗaya. Ya tambayi dalilin da ya sa Obasanjo ya jira sai bayan rasuwar Na’Abba kafin ya fito da irin wannan zargi, yana mai cewa hakan zai ba marigayin damar tabbatarwa ko ƙaryata batun ba. Haka kuma ya tambayi dalilin da ya sa ba a gurfanar da shi a kotu ba a lokacin idan da gaske akwai hujjojin da ke tabbatar da zargin.
Atiku ya kuma yi zargin cewa an yi wannan magana ne domin ɓata masa suna gabanin zaɓen 2027, tare da ba wa ɗan takarar da Obasanjo ke goyon baya wata fa’ida ta siyasa. Ya ce saɓanin da ke tsakaninsu ya samo asali ne daga adawarsa da yunƙurin wa’adi na uku da ake zargin Obasanjo ya yi, yana mai jaddada cewa ya tsaya tsayin daka wajen kare kundin tsarin mulki.
Ya ƙara da cewa ƴan Nijeriya sun fi damuwa da matsalolin tattalin arziƙi, da rashin tsaro, da rashin aikin yi da hauhawar bashin ƙasa fiye da taƙaddamar siyasar da ta faru fiye da shekaru ashirin da suka gabata.














