Babban Hafsan ƴansandan Nijeriya, Olatunji Disu, ya ba jami’an ‘yansanda umarnin harbe duk wanda aka kama yana yawo da makami na haram ko ba bisa ƙa’ida ba. Matakin ya zo ne a matsayin tsaurara yaƙi da matsalar tsaro da ke sake tsamari a sassa daban-daban na ƙasar.
Sufeto Disu ya bayar da wannan umarni ne a ranar Juma’a yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Gidan Gwamnati da ke Makurdi, fadar jihar Benue.
A cewar Shugaban ‘Yansandan, wannan tsattsauran mataki ya biyo bayan umarnin kai tsaye daga Shugaba Bola Ahmed Tinubu, na cewa dole ne a kawo ƙarshen rikici da fitintinun tsaro da ke addabar Jihar Benue da sauran shiyyoyi.
- Tushen Doka (Force Order 237): IG Disu ya bayyana cewa jami’an ‘yansanda sun samu cikakken iko ƙarƙashin tsarin dokar Force Order 237 na yin amfani da ƙarfin makami domin kare kai da al’umma ba tare da jiran sai an sake ba su umarni daga na gaba da su ba.
- Daƙile Asarar Rayukan Jami’a: Shugaban ‘yansandan ya bayyana cewa rundunar ta gaji da asarar rayukan jami’anta, da sojoji, da sauran ma’aikatan tsaro da ke mutuwa a hannun ‘yan ta’adda da tsageru.
“Ba za ku iya yawo a sake ba tare da makamai a hannunku kamar babu doka da oda a ƙasar nan ba. Ba za mu sake zuba ido ana haka ba.” — IGP Olatunji Disu
Babban hafsan ya yi kira ga mazauna Jihar Benue da ma Nijeriya baki ɗaya da su ba jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar samar da ingantattun bayanai na sirri. Ya jaddada cewa babu yadda jami’an tsaro za su sami nasara ba tare da goyon bayan al’umma ba.
Jihar Benue na ɗaya daga cikin jihohin da ke yawan fuskantar hare-haren ‘yan bindiga da tashin hankali tsakanin manoma da makiyaya, wanda ya haifar da asarar rayuka masu yawa da kuma raba dubban jama’a da muhallansu.














