ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

by Rabi'u Ali Indabawa
7 hours ago
Ambaliya

Sabuwar fargabar ambaliya ta mamaye al’ummomi a sassan Nijeriya bayan da Gwamnatin Tarayya ta sanya jihohi 28 da Babban Birnin Tarayya (FCT) cikin jerin yankunan da ke cikin hadarin ambaliya, tana mai gargadin cewa miliyoyin mutane a Arewa da Kudancin kasar na iya fuskantar mummunar ambaliya yayin da ake ci gaba da samun ruwan sama mai karfi.

Gargadin, wanda Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya ta fitar ta hannun Cibiyar Gargadin Farko Kan Ambaliya ta Kasa (National Flood Early Warning Systems Centre), ya shafi lokacin daga 19 ga Yuli zuwa 1 ga Agusta, 2026.

Hukumomin sun yi gargadin cewa ci gaba da ruwan sama, cikar kasa da ruwa, cikar koguna da kuma rashin iya daukar ruwa da magudanan ruwa ke yi na iya haddasa mummunar ambaliya ga daruruwan al’ummomi.

ADVERTISEMENT

Ko da yake jihohin Arewa da ke bakin manyan koguna na cikin hadari, sabon hasashen ya nuna cewa jihohin Kudancin Nijeriya ma za su fuskanci barazana, musamman manyan birane, yankunan bakin teku da kuma al’ummomin da ke kusa da koguna, inda ake sa ran za a fuskanci ambaliyar gaggawa da cikar koguna.

Jihohin da aka bayyana suke cikin mafi girman hadarin ambaliya sun hada da Abia, Adamawa, Akwa Ibom, Anambra, Bayelsa, Benuwe, Cross Riber, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Kwara, Legas, Neja, Ogun, Ondo, Osun, Oyo, Ribers da Taraba.

LABARAI MASU NASABA

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Gwamnatin Tarayya ta kuma bayyana wasu manyan birane da cibiyoyin kasuwanci a Kudancin kasar da ke cikin hadari, ciki har da Legas, Lekki, Ikorodu, Agege, Apapa, Eti-Osa, Ikeja, Surulere, Badagry da Lagos Island a Jihar Legas.

A yankin Kudu maso Gabas, wuraren da ke cikin hadarin ambaliya sun hada da Aba, Umuahia, Ariaria Market, Arochukwu, Onitsha, Fegge, Bridge Head, Awka, Nnewi, Nkpor, Obosi, Anambra West, Ayamelum, Omor, Nzam, Abakaliki, Afikpo, Enugu, Nsukka, Owerri da Orlu.

Haka kuma, a yankin Kudu maso Kudu, an yi gargadi ga Yenagoa, Brass, Nembe, Kaiama, Ogbia, Sagbama, Ekeremor da Kolokuma/Opokuma a Bayelsa; Fatakwal, Bonny, Okrika, Ahoada, Omoku, Eleme, Degema da Bonny Island a Ribers; Warri, Asaba, Sapele, Ughelli, Bomadi, Burutu, Patani da Escrabos a Delta; da kuma Calabar, Bakassi, Ikom, Ogoja da Ugep a Cross Riber.

Gargadin ya kuma shafi wasu al’ummomi a Akwa Ibom, Edo, Ondo, Ogun, Osun, Oyo da Ekiti, inda ake sa ran ambaliyar birane da cikar hanyoyin ruwa za su yi barazana ga gidaje, kasuwanci, gonaki da muhimman ababen more rayuwa.

A yankin Arewa ta Tsakiya, hukumomi sun yi gargadin cewa al’ummomin Lakwaja, Ajaokuta, Idah da Ibaji a Kogi; Makurdi, Agatu, Buruku, Guma da Logo a Benuwe; da kuma Minna, Mokwa, Shiroro, Suleja da Bida a Jihar Neja na cikin babban hadari sakamakon hauhawar matakin ruwa a koguna da kuma kasancewarsu a filayen ambaliya.

Hasashen ya kuma nuna cewa al’ummomin da ke bakin koguna a Yola, Mubi, Song, Ganye a Adamawa da Jalingo, Karim Lamido, Takum da Wukari a Taraba na iya fuskantar mummunar ambaliya idan ruwan sama.

Baya ga yankunan da aka bayyana suna cikin matsanancin hadari, Ma’aikatar ta sanya Adamawa, FCT, Kebbi, Nasarawa, Filato da wasu sassan Taraba cikin yankunan da ke cikin babban hadari da ke bukatar sa ido sosai.

Haka kuma, an sanya al’ummomi 531 a jihohin Bauchi, Borno, Gombe, Jigawa, Kaduna, Kano, Katsina, Sakkwato, Yobe da Zamfara cikin jerin yankunan da ke cikin matsakaicin hadarin ambaliya.

Ma’aikatar ta danganta wannan hadari da yawan ruwan sama, cikar kasa da ruwa, kwararar ruwa a sama cikn kasa, cikar magudanan ruwa da kuma tashin matakan ruwa a koguna. Ta yi gargadin cewa wadannan yanayi na iya haddasa ambaliyar gaggawa, musamman a kananan wurare da manyan biranen da ke da yawan jama’a.

Ta shawarci mazauna yankunan da ke bakin koguna, filayen ambaliya, wuraren dausayi da kusa da magudanan ruwa da su kasance cikin shiri, tana mai gargadin cewa ruwa na iya zuwa cikin kankanin lokaci ba tare da wata ishara ba.

Gwamnatin Tarayya ta kuma umarci Hukumomin Ba da Agajin Gaggawa na Jihohi (SEMA), kananan hukumomi, jami’an muhalli da masu sa ido kan ambaliya a al’umma da su kara sanya ido kan koguna, gadoji, magudanan ruwa da wuraren da ke fuskantar zaizayar kasa.

An kuma shawarci al’ummomin da aka sanya cikin matsanancin hadari da su fara shirye-shiryen kwashe jama’a idan bukatar hakan ta taso, su kare marasa karfi, su guji zama ko kasuwanci a filayen ambaliya, sannan su bi duk wani umarnin gaggawa da hukumomi suka bayar.

Ma’aikatar ta yi kira da a gaggauta share magudanan ruwa, a ci gaba da sa ido kan yawan ruwan sama da matakin ruwa, tare da kai rahoton duk wata alamar samun yawaitar ruwa cikin gaggawa.

Ta kuma jaddada cewa ya kamata a rika hada hasashen ambaliya da yanayin da ake gani a wurare, yadda magudanan ruwa da koguna ke gudana, da kuma umarnin hukumomin agajin gaggawa yayin da ake ci gaba da sa ido kan sauyin yanayi a fadin kasar.

Ambaliya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

MASU ALAKA

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Next Post
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

LABARAI MASU NASABA

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

July 25, 2026
Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

July 25, 2026
Ambaliya

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026
Ambaliya

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Ambaliya

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Ambaliya

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.