ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

by Yusuf Shuaibu
55 minutes ago
ADC

Jam’iyyar ADC ta ce manufofin tattalin arzikin gwamnatin Shugaban kasa, Bola Tinubu sun lalata rayuwar ‘yan Nijeriya a cikin shekaru uku da suka gabata.

ADC ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar, ya ce rahotannin baya-bayan nan na Bankin Duniya da suka nuna cewa mutane miliyan 139 a Nijeriya yanzu suna rayuwa ciki talauci a kasar, shaida ce ta tasirin manufofin gwamnati.

Jam’iyyar ta bayyana cewa akwai shaidar cewa abubuwa za su kara tabarbarewa a kasar idan aka sake zaban Shugaba Tinubu a karo na biyu a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

“ADC na matukar damuwa da rahotannin da Bankin Duniya ya fitar kwanan nan wanda ke nuna cewa mutane miliyan 139 a Nijeriya ko kusan kashi 60 cikin dari na yawan al’umma yanzu suna rayuwa cikin talauci a kasa.

“Wannan ba abin mamaki ba ne, domin wannan mummunan yanayin sakamakon sun faru ne sakamakon manufofin tattalin arziki da suka fifita samun kudade fiye da ceto rayuwar al’ummar Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

“Jam’iyyar ADC ta sha yin gargadin cewa ci gaban tattalin arziki da kara kudaden shiga, da karuwar ajiyar kudin waje da gwamnatin APC karkashin Tinubu ke ci gaba da yin murna da su ba su da amfani idan ba su haifar da ingantaccen rayuwa ga mutane ko kare hanyoyin dogaro da kai ba,” in ji jam’iyyar adawa.

ADC, wanda ta zargi gwamnatin tarayya da nuna sakaci wajen janyo kwancin tattalin arziki da matsin rayuwa a Nijeriya. Ta ce abin da kasar ke bukata shi ne, shugaban kasa wand gwamnatinsa da gaske ta fahimci yadda mutane ke ji kuma take kula da su da gaske.

“Shaidar mutane miliyan 139 da ke cikin talauci da miliyan 17 da ke hadarin yunwa shi ne sakamakon gwamnatin Shugaba Tinubu. Bisa wannan gazawa mai muni kadai, Shugaba Tinubu ya kamata ya yi tunanin yin murabus daga ofis maimakon neman sake zaben sa.”

“Abin da Nijeriya ke matukar bukata shi ne, shugaban da gwamnatinsa da suka fahimci yadda mutane ke ji kuma suke kula da su da gaske. Gwamnati da ta fahimci cewa ainihin ma’aunin kowace manufar tattalin arziki shi ne inganta rayuwar mutane ba wai kara musu wahala ba. Shugaba wanda gwamnatinsa ba ta ci gaba da jin dadin kanta yayin da take rokon mutane su ci gaba da azumi, da kuma gwamnati da ba ta azurta kanta wajen bai wa mutane tallafi.

“Shi ya sa ADC ta yi watsi da hanyoyin rage radadi na wacin gadi da martani na gaggawa da suka zama alamar manufofin tattalin arzikin APC a karkashin shirin tallafin al’umma. Ba za a iya yaki  da talauci ta hanyar kayayyakin rage wahala kawai ba. Ana iya yaki da talauci ta hanyar gina tattalin arziki da zai bai wa ‘yan Nijeriya damar samar da karin abinci, samun albashi mai kyau, da rayuwa cikin farin ciki da daraja,” in ji sanarwar.

ADC ta yi alkawarin cewa gwamnatinta za ta aiwatar da gyare-gyare da za su magance tushen yunwa, rage farashin makamashi da tabbatar da tsaron al’ummomin manoma har ma da kara yawan samar da abinci a cikin gida, da sauran abubuwa.

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

MASU ALAKA

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
Tambarin Dimokuradiyya

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Next Post
ADC

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

LABARAI MASU NASABA

ADC

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.