Jam’iyyar ADC ta ce manufofin tattalin arzikin gwamnatin Shugaban kasa, Bola Tinubu sun lalata rayuwar ‘yan Nijeriya a cikin shekaru uku da suka gabata.
ADC ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar, ya ce rahotannin baya-bayan nan na Bankin Duniya da suka nuna cewa mutane miliyan 139 a Nijeriya yanzu suna rayuwa ciki talauci a kasar, shaida ce ta tasirin manufofin gwamnati.
Jam’iyyar ta bayyana cewa akwai shaidar cewa abubuwa za su kara tabarbarewa a kasar idan aka sake zaban Shugaba Tinubu a karo na biyu a zaben 2027.
“ADC na matukar damuwa da rahotannin da Bankin Duniya ya fitar kwanan nan wanda ke nuna cewa mutane miliyan 139 a Nijeriya ko kusan kashi 60 cikin dari na yawan al’umma yanzu suna rayuwa cikin talauci a kasa.
“Wannan ba abin mamaki ba ne, domin wannan mummunan yanayin sakamakon sun faru ne sakamakon manufofin tattalin arziki da suka fifita samun kudade fiye da ceto rayuwar al’ummar Nijeriya.
“Jam’iyyar ADC ta sha yin gargadin cewa ci gaban tattalin arziki da kara kudaden shiga, da karuwar ajiyar kudin waje da gwamnatin APC karkashin Tinubu ke ci gaba da yin murna da su ba su da amfani idan ba su haifar da ingantaccen rayuwa ga mutane ko kare hanyoyin dogaro da kai ba,” in ji jam’iyyar adawa.
ADC, wanda ta zargi gwamnatin tarayya da nuna sakaci wajen janyo kwancin tattalin arziki da matsin rayuwa a Nijeriya. Ta ce abin da kasar ke bukata shi ne, shugaban kasa wand gwamnatinsa da gaske ta fahimci yadda mutane ke ji kuma take kula da su da gaske.
“Shaidar mutane miliyan 139 da ke cikin talauci da miliyan 17 da ke hadarin yunwa shi ne sakamakon gwamnatin Shugaba Tinubu. Bisa wannan gazawa mai muni kadai, Shugaba Tinubu ya kamata ya yi tunanin yin murabus daga ofis maimakon neman sake zaben sa.”
“Abin da Nijeriya ke matukar bukata shi ne, shugaban da gwamnatinsa da suka fahimci yadda mutane ke ji kuma suke kula da su da gaske. Gwamnati da ta fahimci cewa ainihin ma’aunin kowace manufar tattalin arziki shi ne inganta rayuwar mutane ba wai kara musu wahala ba. Shugaba wanda gwamnatinsa ba ta ci gaba da jin dadin kanta yayin da take rokon mutane su ci gaba da azumi, da kuma gwamnati da ba ta azurta kanta wajen bai wa mutane tallafi.
“Shi ya sa ADC ta yi watsi da hanyoyin rage radadi na wacin gadi da martani na gaggawa da suka zama alamar manufofin tattalin arzikin APC a karkashin shirin tallafin al’umma. Ba za a iya yaki da talauci ta hanyar kayayyakin rage wahala kawai ba. Ana iya yaki da talauci ta hanyar gina tattalin arziki da zai bai wa ‘yan Nijeriya damar samar da karin abinci, samun albashi mai kyau, da rayuwa cikin farin ciki da daraja,” in ji sanarwar.
ADC ta yi alkawarin cewa gwamnatinta za ta aiwatar da gyare-gyare da za su magance tushen yunwa, rage farashin makamashi da tabbatar da tsaron al’ummomin manoma har ma da kara yawan samar da abinci a cikin gida, da sauran abubuwa.














