An yi taro kan cinikayya tsakanin kasashen Sin da Afrika ta Kudu a birnin Cape Town, inda kamfanonin bangarorin biyu suka tattauna kan hadin gwiwa a bangarorin da suka hada da aikin gona da kere-kere da makamashi da hakar ma’adinai da hada-hadar kudi da kera motoci da harkokin jigila.
Majalisar bunkasa cinikayya da kasa da kasa ta kasar Sin (CCPIT) da sashen kula da harkokin cinikayya da masana’antu da takara na Afrika ta Kudu ne suka shirya taron wanda ya samu mahalarta sama da 350.
Mataimakin shugaban Afrika ta Kudu Paul Mashatile, ya ce shirin yarjejeniyar hadin gwiwa kan tattalin arziki domin ci gaba na bai daya da aka cimma tsakanin kasashen biyu, zai rage kudin da kamfanonin Sin ke kashewa wajen shigar da kayayyakin Afrika ta Kudu zuwa Sin, yayin da zai kuma bude sabbin hanyoyin da masana’antun Afrika ta Kudun za su fadada shiga kasuwannin ketare da karfafa takara.
Shugaban majalisar CCPIT Ren Hongbin ya ce manufar taron ita ce, taimaka wa ‘yan kasuwar kasashen biyu fadada hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya da inganta hade ayyukan masana’antu da cimma moriyar juna a bangarori da fannoni daban daban. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post