ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fitar Da Naira Biliyan 250 Domin Bai Wa Manoma Rance

by Sulaiman
2 months ago
Manoma

A ci gaba da kokarin da ta ke yi, gwamnatin tarayya ta fitar da kimanin naira biliyan 250, domin bai wa manoman kasar nan rancen kudi domin yin noma.

Kazalika, gwamnatin ta kuma fitar da kimanin buhunhunan Takin Zamani miliyan 2.15, da nufin tallafa wa manoman kasar, musamman domin a kara bunkasa samar da wadataccen abinci.

  • Hukumar NPA Ta Karrama Jajirtattun Matan Da Ke Aiki A Hukumar
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Kaucewa Takara Mai Hadari

Karamin Minista a ma’aikatar bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, ya sanar da hakan a wata tattaunawa da ya yi da jaridar Business Daily.

ADVERTISEMENT

Ministan ya bayyana cewa, wannan daukin na daga cikin matakan da gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ke ci gaba da dauka, musamman domin magance matsalar samar da wadataccen abinci a kasar da kuma kalubalen da fannin aikin noma a kasar ke fuskanta.

“Wadannan tsare-tsaren da gwamnatin ta samar da su, na ci gaba da tafiya, yadda ya dace, sannan kuma gwamnatin ta fara wanzar da daukar matakan gaggawa kan samar da wadataccen abinci a kasar ne, tun bayan da shugaban kasa a shekarar 2023, ya ayyana dokar ta baci, a fannin na aikin noma na kasar nan,” a cewarsa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

“Mun tafi ne kai tsaye, a kan shirye-shiyen da muke yi tare da yakinin cewa, za su taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin aikin noma a kasar ciki har da noman rani,”in ji ministan.

Ministan ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta kuma rungumi tsarin ganin ana yin noma a kasar har zuwa na tsawon shekara daya, musamman da nufin kara samar da wadataccen abinci a kasar nan.

“A wajen yanzu, batun yin noma a kasar ya wuce kawai yin noma a lokacin damina ko kuma a lokacin rani, amma tsarin a yanzu shi ne, yin noman har na tsawon shekara daya” in ji Abdullahi.

Har ila yau, ya yi nuni da cewa; batun samar da wadataccen abinci a kasar, ya wuce maganar yin noman shi kan shi, amma batu ne da ke nufin samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar.

Kazalika, ministan ya yi nuni da cewa; duk da damuwar karin farashin kayan abinci a daukacin kasuwanin kasar, amma har yanzu ana ci gaba da samun wadataccen abinci a kasar.

“Duk kasuwar da ka shiga a daukacin fadin kasar nan, zai yi wuya ka ga babu kayan abincin da ake sayarwa, akwai wadaccen abinci sai dai kawai a ce babu kudin saya, wannan shi ne kwai babban kalubalen, amma duk da haka, gwamnatin ba ta yi kasa a guiwa ba, domin kuwa ta mayar da hankali wajen rage farashin wasu amfanin gona, domin ‘yan kasar su saya a farashi mai rahusa,” in ji Ministan. “Mun gano amfanin gonar da muka san cewa; ‘yan kasar nan sun fi yin amfani da shi a daukacin fadin kasar, musamman Rogo wanda aka fi yawan amfani da shi a fadin kasar, sai kuma Shinkafa da Masara da Alkama'” a cewar ministan.

Ya kara da cewa, kayan lambu kamar irin su Tumatir da Tattasai da Albasa, an sanya su a cikin jerin kayan da ake samun hauhawar farashinsu, saboda bukatarsu da ake da ita ta yau da kullum.

Abdullahi ya sanar da cewa, ma’aikatar a kwanakin baya, ta samar wa manoman Tumatir dauki, musamman manoman da suke a Jihar Kano, wadanda cutar Tuta absoluta ta lalata gonakinsu na Tumatir.

Kan batun shigo da kayan abinci cikin kasar, ministan ya bayyana cewa; ta dauki wannan matakin na wucin gadi ne, domin daidaita farashin kayan abinci a kasar.

“Misali, bukatar da ake da ita a kasar ta Masara, ta kai ta kimanin tan miliyan 25.

Ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya a karkashin shirin aikin noma na babban bankin Nijeriya (CBN), ta amince da a fitar da buhunhunan Takin Zamni kimanin miliyan 2.15, musamman domin a rage tsadar aikin noma a tsakanin manoman kasar.

Manoma
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Tir Da Hare-haren Amurka Da Isra’ila Kan Wata Makaranta A Iran

Kasar Sin Ta Yi Tir Da Hare-haren Amurka Da Isra’ila Kan Wata Makaranta A Iran

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.