ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fitar Da Naira Biliyan 250 Domin Bai Wa Manoma Rance

by Sulaiman
4 months ago
Manoma

A ci gaba da kokarin da ta ke yi, gwamnatin tarayya ta fitar da kimanin naira biliyan 250, domin bai wa manoman kasar nan rancen kudi domin yin noma.

Kazalika, gwamnatin ta kuma fitar da kimanin buhunhunan Takin Zamani miliyan 2.15, da nufin tallafa wa manoman kasar, musamman domin a kara bunkasa samar da wadataccen abinci.

  • Hukumar NPA Ta Karrama Jajirtattun Matan Da Ke Aiki A Hukumar
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Kaucewa Takara Mai Hadari

Karamin Minista a ma’aikatar bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, ya sanar da hakan a wata tattaunawa da ya yi da jaridar Business Daily.

ADVERTISEMENT

Ministan ya bayyana cewa, wannan daukin na daga cikin matakan da gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ke ci gaba da dauka, musamman domin magance matsalar samar da wadataccen abinci a kasar da kuma kalubalen da fannin aikin noma a kasar ke fuskanta.

“Wadannan tsare-tsaren da gwamnatin ta samar da su, na ci gaba da tafiya, yadda ya dace, sannan kuma gwamnatin ta fara wanzar da daukar matakan gaggawa kan samar da wadataccen abinci a kasar ne, tun bayan da shugaban kasa a shekarar 2023, ya ayyana dokar ta baci, a fannin na aikin noma na kasar nan,” a cewarsa.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

“Mun tafi ne kai tsaye, a kan shirye-shiyen da muke yi tare da yakinin cewa, za su taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin aikin noma a kasar ciki har da noman rani,”in ji ministan.

Ministan ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta kuma rungumi tsarin ganin ana yin noma a kasar har zuwa na tsawon shekara daya, musamman da nufin kara samar da wadataccen abinci a kasar nan.

“A wajen yanzu, batun yin noma a kasar ya wuce kawai yin noma a lokacin damina ko kuma a lokacin rani, amma tsarin a yanzu shi ne, yin noman har na tsawon shekara daya” in ji Abdullahi.

Har ila yau, ya yi nuni da cewa; batun samar da wadataccen abinci a kasar, ya wuce maganar yin noman shi kan shi, amma batu ne da ke nufin samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar.

Kazalika, ministan ya yi nuni da cewa; duk da damuwar karin farashin kayan abinci a daukacin kasuwanin kasar, amma har yanzu ana ci gaba da samun wadataccen abinci a kasar.

“Duk kasuwar da ka shiga a daukacin fadin kasar nan, zai yi wuya ka ga babu kayan abincin da ake sayarwa, akwai wadaccen abinci sai dai kawai a ce babu kudin saya, wannan shi ne kwai babban kalubalen, amma duk da haka, gwamnatin ba ta yi kasa a guiwa ba, domin kuwa ta mayar da hankali wajen rage farashin wasu amfanin gona, domin ‘yan kasar su saya a farashi mai rahusa,” in ji Ministan. “Mun gano amfanin gonar da muka san cewa; ‘yan kasar nan sun fi yin amfani da shi a daukacin fadin kasar, musamman Rogo wanda aka fi yawan amfani da shi a fadin kasar, sai kuma Shinkafa da Masara da Alkama'” a cewar ministan.

Ya kara da cewa, kayan lambu kamar irin su Tumatir da Tattasai da Albasa, an sanya su a cikin jerin kayan da ake samun hauhawar farashinsu, saboda bukatarsu da ake da ita ta yau da kullum.

Abdullahi ya sanar da cewa, ma’aikatar a kwanakin baya, ta samar wa manoman Tumatir dauki, musamman manoman da suke a Jihar Kano, wadanda cutar Tuta absoluta ta lalata gonakinsu na Tumatir.

Kan batun shigo da kayan abinci cikin kasar, ministan ya bayyana cewa; ta dauki wannan matakin na wucin gadi ne, domin daidaita farashin kayan abinci a kasar.

“Misali, bukatar da ake da ita a kasar ta Masara, ta kai ta kimanin tan miliyan 25.

Ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya a karkashin shirin aikin noma na babban bankin Nijeriya (CBN), ta amince da a fitar da buhunhunan Takin Zamni kimanin miliyan 2.15, musamman domin a rage tsadar aikin noma a tsakanin manoman kasar.

Manoma
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Tir Da Hare-haren Amurka Da Isra’ila Kan Wata Makaranta A Iran

Kasar Sin Ta Yi Tir Da Hare-haren Amurka Da Isra’ila Kan Wata Makaranta A Iran

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.