Mutum biyar sun rasa rayukansu sakamakon ɓarkewar cutar ƙwalara a Filato, yayin da hukumomin lafiya suka tabbatar da wasu sun kamu da cutar har su 11 a wasu sassan jihar.
Rahotanni sun nuna cewa annobar ta fara jefa fargaba a tsakanin al’umma, musamman a yankunan da abin ya fi ƙamari.
Hukumar lafiya ta jihar ta ce an fara ɗaukar matakan gaggawa domin daƙile yaɗuwar cutar, ciki har da wayar da kan jama’a kan tsaftar muhalli, da tsaftatace ruwa da kuma muhimmancin garzayawa asibiti idan an ga alamun cutar.
Jami’an lafiya sun bayyana cewa ƙwalara cuta ce mai saurin yaɗuwa ta hanyar gurbataccen ruwa ko abinci, kuma tana haddasa amai da gudawa mai tsanani wanda kan jawo rashin ruwa a jiki cikin ƙanƙanin lokaci.
Mahukunta sun buƙaci mazauna jihar su kula da tsafta, su riƙa wanke hannu akai-akai tare da kauce wa shan ruwan da ba a tabbatar da tsaftarsa ba domin rage yaɗuwar annobar.















Discussion about this post