Aƙalla mata 600 ne aka yi wa gwajin cutar sankarar mama a Jihar Katsina, yayin da aka gudanar da tiyata ga guda 50 domin ceton rayukan masu fama da cutar a wani shirin jinya kyauta da aka gudanar a jihar.
Uwargidan Gwamnan Jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Radda, ta ce shirin wani ɓangare ne na yarjejeniyar haɗin gwuiwa ta shekaru biyar tsakanin gwamnatin jihar da abokan hulɗa domin inganta gano cutar da wuri da kuma sauƙaƙa samun magani ga mata. Ta bayyana cewa an gudanar da shawarwarin lafiya sama da 800 a yayin shirin.
Gwamna Dikko Umaru Radda ya yi kira ga masu hannu da shuni, da ƙungiyoyin ci gaba da kamfanoni masu zaman kansu da su mara wa ƙoƙarin yaƙi da cutar baya, yana mai cewa gwamnati kaɗai ba za ta iya magance irin waɗannan manyan ƙalubalen lafiya ba.
Ya kuma yaba wa tawagar Revive Mission Belgium da Pledging Aid Charity Foundation bisa gudunmawar da suka bayar, yana mai jaddada cewa haɗin gwuiwa irin wannan zai taimaka wajen rage mace-macen da cutar sankarar mama ke haddasawa a jihar.















Discussion about this post