Hukumar ƙwallon ƙafa ta Tunisia ta sallami kocin tawagar ƙasar, Sabri Lamouchi, bayan mummunan kashin da tawagarsa ta sha da ci 5-1 a hannun Sweden a wasan farko na gasar Kofin Duniya ta 2026.
Rahotanni sun ce an ɗauki matakin ne bayan ganawar gaggawa da jami’an hukumar suka yi. Tunisia ta nuna rauni sosai a wasan, inda ‘yan wasan Sweden suka mamaye fili tare da jefa ƙwallaye biyar, lamarin da ya jefa magoya baya cikin fushi da takaici.
Kafin wannan lokaci, Tunisia ta kuma sha kashi 5-0 a wasan sada zumunta da Belgium, abin da ya ƙara nuna matsalar tawagar. Lamouchi, wanda aka naɗa a farkon 2026, bai daɗe a muƙamin ba, kuma ana zargin rashin iya haɗa ‘yan wasa da gazawar dabarunsa ne ya janyo masa matsin lamba.
Rahotanni sun kuma nuna cewa an samu rikici a sansanin tawagar bayan wasan. Yanzu Tunisiyya za ta nemi sabon koci cikin gaggawa domin ceton burinta a gasar, musamman gabanin wasanta na gaba da Japan a rukuni na F.















Discussion about this post