Tsohon Hafsan Sojin Nijeriya, Tukur Buratai mai ritaya, ya yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki matakin gaggawa kan matsalar tsaro ba, Ministoci, da Sanatoci da gwamnoni na iya zama sabbin hari na ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda a Nijeriya.
Buratai ya bayyana hakan ne bayan kisan Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya a hannun ‘yan bindiga, yana mai cewa wannan lamari alama ce ta yadda matsalar tsaro ke ƙara tsananta. A cewarsa, idan har babban jami’in soja zai faɗa hannun masu laifi, hakan na nuna cewa barazanar tsaro ta kai wani mataki mai hatsari.
Ya ce tun a 2021 ya yi hasashen cewa matsalar ta’addanci da ‘yan bindiga na iya ɗaukar tsawon shekaru 20 idan ba a ɗauki tsauraran matakai ba. Buratai ya buƙaci a ƙara ƙarfafa tsaron manyan jami’an gwamnati tare da inganta tattara bayanan sirri da yaƙi da hanyoyin da masu laifi ke samun goyon baya.
Buratai ya jaddada cewa yaƙi da rashin tsaro ba aikin sojoji kaɗai ba ne, yana mai kira ga gwamnati, da al’umma da hukumomin tsaro su haɗa kai domin daƙile matsalar kafin ta ƙara muni.














Discussion about this post