Rundunar ƴansanda ya ƙasa reshen jihar Binuwe ta tabbatar da kashe wasu da ake zargin ƴan bindiga ne su uku a wata musayar wuta da jami’anta suka fafata da su yayin wani sumame da aka gudanar a Jihar Benue.
Kakakin rundunar a jihar, DSP Edet Udeme, ta ce an samu nasarar ne tsakanin 6 zuwa 12 ga Yuni ta hanyar sintiri da kuma bayanan sirri da aka samu daga al’umma. Ta ce jami’an rundunar tare da ƴan sa-kai sun kai ɗauki bayan samun rahoton motsin ƴan bindiga a hanyar Vaase–Chito da ke ƙaramar hukumar Ukum.
A cewarta, ƴan bindigar sun buɗe wa jami’an tsaro wuta, lamarin da ya haddasa musayar wuta mai zafi, inda aka kashe uku daga cikinsu. Rundunar ta kuma ƙwato bindigar AK-47 guda ɗaya, da harsasai 21 da babur ɗaya daga hannunsu, yayin da sauran suka tsere da raunukan harbi.
Ƙwamishinan ƴansandan jihar ya yabawa jami’an da suka gudanar da aikin, tare da buƙatar al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin taimakawa yaƙi da ƴan bindiga da sauran masu aikata laifuka.















Discussion about this post