Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci INEC da ta soke rajistar ADC da wasu jam’iyyun siyasa huɗu bisa zargin gaza cika sharuɗɗan kundin tsarin mulki na ci gaba da kasancewa a matsayin jam’iyyun siyasa.
Sauran jam’iyyun da hukuncin ya shafa sun haɗa da Action Peoples Party (APP), da Action Alliance (AA), da Accord Party (AP) da Zenith Labour Party (ZLP). Mai shari’a Peter Lifu ne ya yanke hukuncin bayan sauraron ƙarar da Inuwar tsofaffin ƴan majalisu ta shigar.
Masu ƙarar sun kafa hujjar cewa jam’iyyun sun kasa kai matakin nasarar zabe da sashi na 225A na kundin tsarin mulki ya tanada, ciki har da lashe kujera ko samun kaso 25% na ƙuri’u a matakin da doka ta tanada.
Sun ce ci gaba da barin irin waɗannan jam’iyyu na ƙara ɗawainiya ga tsarin zaɓe da takardun kaɗa kuri’a.
Hukuncin na iya girgiza siyasar 2027 matuƙa idan ya tabbata, musamman ganin ADC na daga cikin jam’iyyun da manyan ‘yan adawa suka runguma domin ƙalubalantar Bola Ahmed Tinubu a zaɓe mai zuwa.














Discussion about this post