Jam’iyyar ADC ta zaɓi Rotimi Amaechi a matsayin mataimakin ɗan takararta na shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, domin tunkarar babban zaɓen 2027.
Rahotanni sun ce matakin na daga cikin dabarun jam’iyyar na ƙarfafa tikitinta a faɗin ƙasa. Amaechi, tsohon gwamnan Rivers kuma tsohon Ministan Sufuri, ya zo na biyu ne a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar kafin daga bisani a zaɓe shi a matsayin mataimaki
ADC ta ce gogewarsa a mulki da siyasa za su taimaka wajen faɗaɗa karɓuwar tikitin Atiku-Amaechi. Sai dai akwai ruɗani kan batun, domin wasu jami’an jam’iyyar sun ce ba a fitar da sanarwa a hukumance ba tukuna.
Kakakin ADC, Bolaji Abdullahi, ya ce bai da tabbacin labarin a lokacin da aka tuntuɓe shi, duk da cewa rahotanni da dama sun tabbatar da zaɓin.
Zaɓin Amaechi na zuwa ne yayin da ADC ke ƙoƙarin haɗa kan manyan ‘yan adawa domin ƙalubalantar Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyar APC a zaɓen 2027.















Discussion about this post