Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) reshen Jami’ar Jihar Filato, ASUU-PLASU, ta ayyana tsunduma yajin aikin sai baba ta gani, sakamakon gazawar mahukuntan jami’ar wajen magance bukatunta guda shida.
Kungiyar ta sanar da fara yajin aikin ne ranar Laraba, bayan wani taron majalisar kungiyar da ta gudanar sakamakon karewar wa’adin kwanaki 14 da ta bai wa mahukuntan jami’ar a ranar 11 ga Agusta domin su amsa bukatunta.
A cikin wata sanarwa da Shugabar reshen kungiyar, Vincent Choji, da Sakataren ta, Lomka Kopdiya, suka sanya wa hannu, wadda aka rabawa manema labarai ranar Laraba, kungiyar ta ce har yanzu babu ko daya daga cikin bukatunta shida da mahukuntan jami’ar suka magance yadda ya kamata.
Kungiyar ta ce yajin aikin zai ci gaba har sai an dauki matakan da suka dace wajen magance matsalolin da ta gabatar.














