Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC ta yi wa ɗan takarar jam’iyyar APC a mazabar tarayya ta Ise-Orun/Ikere/Ekiti ta Kudu maso Yamma, Injiniya Toyin Zacheous Okoro, tambayoyi kan zargin karya dokokin aikin gwamnati da kuma wasu laifukan da suka shafi cin hanci da rashawa.
Okoro, wanda tsohon Babban Mataimaki ne ga Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya isa shalkwatar ICPC da ke Abuja ranar Alhamis, 17 ga Satumba, bayan gayyatar da hukumar ta aika masa a ranar 7 ga Satumba, 2026. Rahotanni sun ce ya shafe sama da sa’o’i biyu yana amsa tambayoyin masu binciken hukumar kafin a sake shi bisa beli, tare da umarnin sake dawowa domin ci gaba da bincike.
ICPC na binciken zargin cewa Okoro ya ci gaba da gudanar da wani kamfani mai zaman kansa yayin da yake rike da mukamin mataimaki a Majalisar Ƙasa, abin da hukumar ke cewa ya saba wa dokokin aikin gwamnati. Ana kuma zarginsa da yin amfani da matsayinsa na ma’aikacin gwamnati wajen samun kwangiloli ga kamfanin daga hukumomin gwamnati da suka haɗa da Nigerian Ports Authority (NPA), da SMEDAN da NASENI.
Binciken ya kuma shafi zargin cewa Okoro ya ci gaba da karɓar albashi da alawus-alawus daga Majalisar Ƙasa yayin da yake da alaƙa da mallakar kamfanin, da kuma zargin sauya ko mayar da ranar wasikar murabus ɗinsa domin kare kansa daga zarge-zargen. Ana kuma binciken zargin cewa ya gabatar da bayanan da ba daidai ba a takardun da ya miƙa wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).
Ya zuwa lokacin wallafa wannan rahoton, ba a samu martanin Okoro a bainar jama’a kan zarge-zargen ba. ICPC na cigaba da bincike, kuma zarge-zargen da ake yi masa ba su zama hujjar cewa ya aikata laifi ba har sai an tabbatar da hakan ta hanyar da doka ta tanada.














