ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Ta Yi Wa Dan Takarar APC A Ekiti Titsiye Kan Zargin Badakalar Kuɗi

by Abubakar Sulaiman
8 hours ago
ICPC

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC ta yi wa ɗan takarar jam’iyyar APC a mazabar tarayya ta Ise-Orun/Ikere/Ekiti ta Kudu maso Yamma, Injiniya Toyin Zacheous Okoro, tambayoyi kan zargin karya dokokin aikin gwamnati da kuma wasu laifukan da suka shafi cin hanci da rashawa.

Okoro, wanda tsohon Babban Mataimaki ne ga Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya isa shalkwatar ICPC da ke Abuja ranar Alhamis, 17 ga Satumba, bayan gayyatar da hukumar ta aika masa a ranar 7 ga Satumba, 2026. Rahotanni sun ce ya shafe sama da sa’o’i biyu yana amsa tambayoyin masu binciken hukumar kafin a sake shi bisa beli, tare da umarnin sake dawowa domin ci gaba da bincike.

ICPC na binciken zargin cewa Okoro ya ci gaba da gudanar da wani kamfani mai zaman kansa yayin da yake rike da mukamin mataimaki a Majalisar Ƙasa, abin da hukumar ke cewa ya saba wa dokokin aikin gwamnati. Ana kuma zarginsa da yin amfani da matsayinsa na ma’aikacin gwamnati wajen samun kwangiloli ga kamfanin daga hukumomin gwamnati da suka haɗa da Nigerian Ports Authority (NPA), da SMEDAN da NASENI.

ADVERTISEMENT

Binciken ya kuma shafi zargin cewa Okoro ya ci gaba da karɓar albashi da alawus-alawus daga Majalisar Ƙasa yayin da yake da alaƙa da mallakar kamfanin, da kuma zargin sauya ko mayar da ranar wasikar murabus ɗinsa domin kare kansa daga zarge-zargen. Ana kuma binciken zargin cewa ya gabatar da bayanan da ba daidai ba a takardun da ya miƙa wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

Ya zuwa lokacin wallafa wannan rahoton, ba a samu martanin Okoro a bainar jama’a kan zarge-zargen ba. ICPC na cigaba da bincike, kuma zarge-zargen da ake yi masa ba su zama hujjar cewa ya aikata laifi ba har sai an tabbatar da hakan ta hanyar da doka ta tanada.

LABARAI MASU NASABA

Neja: An Fesa Wani Abu A Ɗakin Da Aka Tsare Mu – Matashin Da Ya Tsira

ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

ICPC
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Abubuwa 12 Da Ya Kamata A Sani Kan Abin Da Aka Aika Wa Majalisun Jihohi
  • Abubakar Sulaiman
    Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027
  • Abubakar Sulaiman
    Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis
  • Abubakar Sulaiman
    Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja
Manyan Labarai

Neja: An Fesa Wani Abu A Ɗakin Da Aka Tsare Mu – Matashin Da Ya Tsira

September 18, 2026
ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna
Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

September 18, 2026
Matatar Dangote Za Ta Ƙara Yawan Ma’aikata Da Samar Da Mai
Labarai

Matatar Dangote Za Ta Ƙara Yawan Ma’aikata Da Samar Da Mai

September 18, 2026
Next Post
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Zanga-Zanga Ta Ɓarke A Minna

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Zanga-Zanga Ta Ɓarke A Minna

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Neja: An Fesa Wani Abu A Ɗakin Da Aka Tsare Mu – Matashin Da Ya Tsira

September 18, 2026
ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

September 18, 2026
Matatar Dangote Za Ta Ƙara Yawan Ma’aikata Da Samar Da Mai

Matatar Dangote Za Ta Ƙara Yawan Ma’aikata Da Samar Da Mai

September 18, 2026
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Binciken Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja

September 18, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Zanga-Zanga Ta Ɓarke A Minna

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Zanga-Zanga Ta Ɓarke A Minna

September 18, 2026
ICPC Ta Yi Wa Dan Takarar APC A Ekiti Titsiye Kan Zargin Badakalar Kuɗi

ICPC Ta Yi Wa Dan Takarar APC A Ekiti Titsiye Kan Zargin Badakalar Kuɗi

September 18, 2026
Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Abubuwa 12 Da Ya Kamata A Sani Kan Abin Da Aka Aika Wa Majalisun Jihohi

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Abubuwa 12 Da Ya Kamata A Sani Kan Abin Da Aka Aika Wa Majalisun Jihohi

September 18, 2026
Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

September 18, 2026
Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

September 18, 2026
Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

September 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.