Hukumomin Jihar Neja sun sanya dokar hana fita na tsawon sa’o’i 24 a Minna, babban birnin jihar, bayan ɓarkewar zanga-zanga a wasu sassan birnin.
Mai bai wa Gwamna Mohammed Umar Bago shawara kan yaɗa labarai, Zayyanu A. Salihu, ne ya sanar da dokar a shafinsa na Instagram.
A cewarsa, dokar ta fara aiki ne bayan sallar Juma’a.
Ya kuma buƙaci mazauna jihar da su mutunta dokar tare da guje wa duk wani abu da zai iya ƙara tayar da hankali.
Wani mazaunin Unguwar Tunga Sabon Titi, inda lamarin ya faru, ya shaida wa manema labarai cewa wasu matasa da suka fusata sun riƙa jifan jami’an tsaro da duwatsu, yayin da ’yansanda suka yi amfani da bindigogi.
Mutumin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ’yansanda sun harbi mutane huɗu, kuma ɗaya daga cikinsu ya mutu nan take.
Tun da farko, jami’ai sun yi zargin cewa wata cuta ce ta haddasa mutuwar wasu matasa da ake zargi da haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba.
Sai dai gwamnatin jihar ta kafa kwamitin bincike domin gano ainihin musabbabin mutuwar matasan.
Bayan faruwar lamarin, Gwamna Bago ya ayyana kwanaki uku na zaman makoki tare da dakatar da yaƙin neman zaɓensa.














