Hukumomin Saudiyya sun ƙi amincewa da buƙatar da Nijeriya ta gabatar na ƙara yawan kason mahajjatan da za su tafi aikin Hajjin shekarar 2027.
Hukumar Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ce ta bayyana hakan, tana mai cewa gwamnatin Saudiyya ta sanar da Nijeriya cewa ba za ta ƙara yawan adadin kujerun da aka ware wa ƙasar ba domin aikin Hajjin 2027.
Buƙatar ƙarin kason na daga cikin matakan da Nijeriya ta ɗauka domin samar da damar samun ƙarin mahajjata daga ƙasar zuwa Saudiyya a kakar Hajjin mai zuwa. Sai dai, hukuncin Saudiyya na nufin Nijeriya za ta gudanar da aikin Hajjin 2027 ne bisa adadin kason da aka riga aka ware mata.
Bayanan NAHCON sun nuna cewa kason Nijeriya na Hajjin 2027 ya kasance mahajjata 50,000: 35,000 na mahajjatan gwamnati, sannan 15,000 na masu zuwa ta hannun kamfanonin yawon buɗe ido masu lasisi. Saudiyya ta ƙi ƙara wannan adadi saboda ƙarancin damar wuraren ibada da kuma tsarin kiyaye kason da aka amince wa kowace ƙasa
NAHCON ta ce tana ci gaba da shirye-shiryen aikin Hajjin 2027, tare da yin aiki da hukumomin Saudiyya da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da gudanar da aikin Hajjin cikin tsari da sauƙi ga alhazan Nijeriya.
Rahoton ya zo ne yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen aikin Hajjin 2027, inda batun yawan kason mahajjata ke daga cikin muhimman abubuwan da ke shafar yadda jihohi da hukumomin alhazai za su tsara tafiyar mahajjatan Nijeriya.














