Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bukaci jama’ar Jihar Adamawa da su goyi bayan gwamnan jihar, Ahmadu Umaru Fintiri, da kyawawan ayyukan ci gaban da gwamnan ke gudanarwa.
Atiku, wanda shi ne dan takarar kujerar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben 2023, ya yi kiran ne ranar Litinin a Yola.
- Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United
- Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa
Ya ci gaba da cewa “Fintiri ya yi abin a zo agani a yaba, musamman ta bangaren ayyukan ci gaba, ilimi da bangaren kiwon lafiya.
“Na yaba wa gwamnatin da irin kyakkyawan nasarorin da ta cimma, musamman ta fuskacin ayyukan ci gaba, ilimi da kiwon lafiya” in ji Atiku.
Wannan ita ce ziyarar tsohon mataimakin shugaban kasar a jihar, tun bayan gudanar da babban zaben 2023, da ya samu tarba daga mataimakiyar gwamnan jihar, Farfesa Kaletapwa Farauta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp