Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa
Ga duk mai bibiyar irin ci gaban da kungiyar BRICS ke samu a shekarun baya bayan nan, ya kwana da...
Ga duk mai bibiyar irin ci gaban da kungiyar BRICS ke samu a shekarun baya bayan nan, ya kwana da...
Yayin da ake gudanar da baje koli na 23 na Sin da ASEAN da taron bangarorin biyu kan kasuwanci da zuba jari, kafar CGTN ta gudanar da wani nazari tsakanin masu bayar da amsa a fadin duniya, inda kaso 90.9 suka yi imanin cewa, ci gaba da karbar bakuncin irin wannan baje koli, ya nuna tsayayyen kudurin Sin na bunkasa bude kofa. Baje kolin na wannan karo ya ja hankalin kamfanoni 3,300, inda ake sa ran masu sayayya 33,000 za su hallara. Cikin nazarin, kaso 89.5 na masu bayar da amsa sun ce baje kolin ba kawai muhimmiyar kafar nuna nasarorin hadin gwiwar Sin da kasashen ASEAN ba ne, wani dandali ne mai muhimmanci na bunkasa musayar kasuwanci da haduwar masana’antu da gabatar da damarmakin ci gaban yankin. An wallafa nazarin ne a dandamalin CGTN na harsunan Ingilishi da Sipaniyanci da Faransanci da Larabci da Rashanci, inda mutane 3950 suka kada kuri’a tare da bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’o’i 24. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
An kammala taro na 13 na dandalin tattauna batutuwan tsaro na Xiangshan, yau Alhamis a birnin Beijing. Taron mai jigon...
A yau Alhamis aka bude bikin baje koli na 23 na Sin da ASEAN da taron tattauna kasuwanci da zuba...
Gwamnatin yankin musammam na Hong Kong na kasar Sin, ta fitar da shirin raya tattalin arziki da zamantakewa na shekaru 5, a jiya Laraba. Wannan shi ne karo na farko da aka fitar da cikakken shiri domin raya tattalin arziki da zamantakewa a yankin na musammam na Hong Kong. Shirin na shekaru 5 ya alamta shigar yankin cikin fagen shugabancin al’umma mai mayar da hankali kan cikakken tsari mai hangen nesa da fada da cikawa. A matsayinsa na wurin da aka fi gudanar da harkokin tattalin arziki cikin ‘yancin a duniya, kuma cibiyar hada-hadar kudi ta duniya, Hong Kong ya zama wata muhimmiyar kasuwa mai tasiri a yankin kudu maso gabashin Asia da yammacin Asia da kudancin Amurka a shekarun baya-bayan nan. Jerin harkokin da suka shafi hada-hadar kudi da cinikayya da matakan kirkire-kirkire da aka zayyana cikin shirin na shekaru biyar-biyar na farko, zai kara karfafa matsayin Hong Kong na cibiyar hulda da hada-hada. Ana sa ran karkashin jagorancin shirin na shekaru biyar-biyar na farko, Hong Kong zai ci gaba da amfani da fifiko na musammam da yake da su na dogaro da babban yankin Sin da hadewa da sassan duniya, domin hawa sabon tafarkin shugabanci da samun wadata. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a wanzar da kwazo domin fadada, da karfafa ci gaban fannin kere-kere, ta yadda za a samar da goyon baya mai karfi ga bunkasa zamanantarwa irin ta kasar Sin. Shugaba Xi, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar zartarwa ta rundunar sojojin kasar Sin, ya yi kiran ne cikin wani umarni da ya bayar a baya-bayan nan, wanda aka gabatar a yayin taron kasa kan batun bunkasa kere-kere, wanda ya gudana jiya Laraba da yau Alhamis a birnin Beijing. Shugaba Xi, ya ce ya kamata a kara azamar tabbatar da ci gaba mai inganci, da tsaro bisa matakin koli, da samar da ci gaba mai kunshe da basira kana marar gurbata yanayi, a kuma mayar da tsarin hada-hadar masana’antun kasar Sin mai karin dogaro da kai da juriyar hadurra. Daga nan sai shugaban na Sin ya jaddada bukatar gaggauta bunkasa zamanantar da tsarin ayyukan masana’antu ta hanyar ingiza kere-kere a matsayin kashin bayan hakan, da karfafa tushen sashen tattalin arziki mai nasaba da sarrafawa, da hada-hadar sayar da hajoji da hidimomi. (Saminu Alhassan)
Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar NDC a Zamfara, Sanata Kabiru Marafa, ya yi alkawarin cewa zai yi murabus idan aka...
Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama wani shahararren mai ƙirƙirar bidiyo a TikTok, Ukasha Yahaya, wanda aka fi sani...
Ana sa ran Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai shiga tsakani domin sasanta rikicin siyasa da ya kunno kai tsakanin...
Rundunar ’Yansandan Jihar Katsina ta dakile wani harin ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Dutsin-Ma, tare da ceto mutane huɗu da...
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.