Babban Hafsan Soja (COAS), Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya sha alwashin shawo kan matsalar tsaro, inda ya ce za su yi dukkan abin yi wajen inganta tsaro, duk da wasu hare-haren da aka kai kwanan nan, a Buni-Gari da ke jihar.
Olufemi ya bayyana haka ne yayin ziyarar karfafa wa sojojin da ke bakin daga a jihar gwiwa a Yobe, inda ya kara da cewa, dangantakarsa da jihar ta musamman ce, wanda a baya ya kasance ya rike matsayin kwamandan Brigade da Sector 2 a jihar.
- Ku Guji Rubuta Rahoton Farfagandar ‘Yan Ta’adda Mai Ɗaukar Hankali – Gwamnati Ga ‘Yan Jarida
- Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
“Mun zo ne a yau musamman don karfafa gwiwar al’ummar jihar Yobe da Sojojin mu da ke aikin samar da tsaro, duk da koma-bayan da muka samu, na sabbin hare-haren Boko Haram.
“Duk da cewa, ba zan iya yin cikakken bayani dangane da sabbin dabarun da muka dauka ba. Amma mutanen Yobe su kwantar da hankalinsu kuma abubuwa za su inganta.”
Har ila yau, ya yi karin haske dangane da wasu muhimman matakan da za a dauka don magance rashin tsaro a jihar, ciki har da tura karin sojoji tare da kayan aikin tsaro.
A nasa bangaren, Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya yaba wa COAS kan daukar matakan gaggawa wajen mayar da martani kan hare-haren kwanan nan, sannan ya yi wa sojojin da suka rasu addu’a.
Ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin farar hula da sojoji, inda ya bukaci karfafa hadin gwiwa wajen bayar da bayanan sirri don dakile matsalolin tsaro.
Gwamna Buni ya kara da cewa, “Dole mu hada kai mu yi aiki tare, tsakanin jami’an hukumomin tsaro wajen bayar da gudummawa tsakanin rundunonin tsaron Nijeriya.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp