Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kebbi, Yakubu Ahmed, ya musanta rahotannin da ke cewa wata sabuwar ƙungiyar ta’addanci mai suna “Sai Malam” ta bayyana a jihar.
Ahmed ya bayyana hakan ne yayin da yake jagorantar wata babbar tawagar kafafen yaɗa labarai domin kai ziyarar girmamawa ga Manajan Darakta na Kamfanin Dillancin labarai na Nijeriya, Ali M. Ali, a Abuja ranar Talata.
Ya bayyana ikirarin a matsayin “ƙarya tsagwaronta” tare da cewa wani yunƙuri ne na yaɗa bayanan ƙarya domin rikita al’umma gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
Kwamishinan ya kuma musanta wani rahoton kafafen yaɗa labarai da ya yi zargin cewa yara fiye da 130 ne ke mutuwa a kullum a jihar sakamakon yawan mace-macen yara, yana mai cewa rahoton ba gaskiya ba ne.
A cewarsa, binciken da hukumomin tsaro suka gudanar ya nuna cewa ƙungiyar da ake kira “Sai Malam” ta ƙunshi wasu matasa da ke aikata laifukan yanar gizo da kuma damfarar mutane ta hanyar intanet.
Ya ce, “Lokacin da aka fitar da wannan bayanin, ya tayar da hankalin kusan kowa. Mun samu kira da yawa daga sassa daban-daban na ƙasar nan da ma ƙasashen waje suna neman tabbatar da sahihancin wannan labari.
“Abin da bincike ya gano shi ne cewa ba ƙungiyar ta’addanci ba ce, sai dai wasu matasa da ke aikata laifukan yanar gizo, suna amfani da kwamfuta wajen tuntuɓar jami’an gwamnati da mutanen da suke zaton suna da kuɗi domin damfararsu.
“An riga an kama wasu daga cikinsu. Su ne dai waɗanda suke kiran kansu “‘Yan Vocal”.
Waɗannan ‘Yan Vocal ne yanzu ake kira da suna Sai Malam.”Kwamishinan ya jaddada cewa hukumomin tsaro na ci gaba da sa ido domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar Kebbi.














