Sakamakon binciken jin ra’ayin mutane 11,521 daga kasashen duniya 41, wanda kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, ya nuna gamsuwa game da yadda tsarin siyasar Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya gabatar da salon Sin na warware matsalar jagorancin siyasa mai mulkin kasa, wanda hakan ya samu matukar karbuwa tsakanin al’ummun kasa da kasa.
A tsarin siyasar yammacin duniya mai tarin jam’iyyu, an fi mayar da hankali ga muradun zabe yayin kada kuri’u, da ingiza rabuwar kawuna tsakanin rukunonin al’umma domin cimma muradun lashe zabe. kuma gajeren wa’adin mulki, kan haifar da kokarin samar da moriyar siyasa ta gaggawa da manufofi masu gajerun wa’adi. Yayin binciken jin ra’ayin jama’a, kaso 63.7 bisa dari na masu bayyana mahanga, sun amince cewa gwagwarmayar neman nasara tsarin jam’iyyu daban daban na gurgunta tsare-tsaren jagorancin kasa.
Dangane da daidaiton manufofi kuwa, kaso 66.3 bisa dari sun amince cewa, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na da ikon dinke bangarorin siyasa mabanbanta, da al’ummun da ma ba sa cikin jam’iyyu wajen cimma muradun bai daya, da samar da kyakkyawar alkibla mai daidaito, da bukatun raya kasa baki daya. (Saminu Alhassan)














