Mataimakin wakilin Sin na dindindin a MDD Sun Lei, a jiya Litinin 6 ga watan Afrilu, ya gabatar da jawabi a babban taron MDD mai taken “shirin gyara tsarin MDD bisa cika shekaru 80 da kafuwarta” (UN80), inda ya bayyana cewa, bangaren Sin yana goyon bayan jawabin da wakilin Uruguay ya yi a madadin “kungiyar 77 da Sin”. Ya yi fatan za a bai wa kasashe masu tasowa muhimmanci yadda ya kamata a cikin gyare-gyaren da za a yi wa tsarin MDD, tare da tattara ra’ayoyin kasashe mambobi yadda ya kamata, da kuma bayyana burikan dukkan kasashe mambobi, ta yadda sakamakon gyare-gyaren zai dace da tarihi.
Sun Lei ya ce, bangaren Sin yana sa ran dukkan kasashe mambobi da sakatariyar MDD su nace ga ainihin manufar gyare-gyaren, su mai da hankali ga yin aiki tukuru, tare da aiwatar da sakamakon da aka riga aka samu, da kuma inganta gyare-gyaren ta hanyar hada kowa da kowa da kuma nuna gaskiya.
Sun Lei ya bayyana cewa, a game da yiwuwar hade asusun yawan al’umma ta MDD da hukumar mata ta MDD, bangaren Sin yana ganin cewa, ya kamata gyare-gyaren su magance damuwa da biyan bukatun kasashe masu amfana da ayyukan da kuma karfafa ingancin ayyuka, tare da aiwatar da muhimman ka’idojin ’yancin kai na kasashe da jagorancinsu yadda ya kamata, tare da tabbatar da cewa an kiyaye ka’idoji da tsare-tsaren aiwatarwa na wadannan hukumomi biyu gaba daya, da kuma taimakawa kasashe masu tasowa wajen aiwatar da manufofin ci gaba mai dorewa masu alaka. (Amina Xu)















Discussion about this post