Masana harkokin shari’a sun bayyana damuwa cewa naɗa Murtala Sule Garo a matsayin Mataimakin Gwamnan Jihar Kano na iya jinkirta shari’ar zargin almundahana ta naira biliyan 57.4 da ake yi masa, sakamakon kariyar doka da kundin tsarin mulki ya tanada ga masu riƙe da wasu manyan mukamai.
Bayan murabus ɗin tsohon mataimakin gwamna, Abdulsalam Gwarzo, sunan Garo ya riƙa yawo a matsayin wanda ake iya maye gurbinsa da shi. A halin yanzu, yana fuskantar shari’a tare da tsohon gwamnan Jihar Kano, Umar Ganduje, da wasu mutum biyu kan zargin karkatar da kuɗaɗen gwamnati har naira biliyan 57.4.
- Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo
- 2027: Ɗan Buhari Ya Bayyana Sha’awar Tsayawa Takarar Majalisar Wakilai
Shari’ar, wadda Gwamnatin Jihar Kano ta shigar, ana kallonta a matsayin ɗaya daga cikin manyan shari’o’in cin hanci da rashawa mafi ɗaukar hankali a jihar a ‘yan shekarun nan.
Da yake zantawa da manema labarai a Kano ranar Talata, wani babban lauya, Usman Bello, ya ce idan har Garo ya karɓi mukamin Mataimakin Gwamna, zai samu kariya a ƙarƙashin Sashe na 308 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya, wanda ke ba wasu masu muƙaman gwamnati kariya daga gurfanar da su a gaban kotu yayin da suke kan mulki.
Ya ce, “Lokacin da ake maganar naɗin ya na da matuƙar muhimmanci, musamman idan aka yi la’akari da girman zarge-zargen da kuma matakin da shari’ar ta kai.”
Haka kuma, Bello Abubakar Ginsau na ƙungiyar Kano Governance and Accountability Forum ya jaddada buƙatar yin taka-tsantsan.
Ya ce, “Ya dace a yi nazari sosai kan lokacin da ake yin irin waɗannan naɗe-naɗe a yayin da ake ci gaba da shari’a. Dole ne a tabbatar da cewa riƙon amana da gaskiya sun kasance ginshiƙai a duk wani mataki da za a ɗauka.”















Discussion about this post