Dakarun rundunar ‘Operation FANSAN YANMA’ sun fafata mummunan artabu da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne a wani samame da ya ɗauki sama da sa’o’i uku a Jihar Zamfara, yayin da har yanzu ba a san yawan waɗanda suka mutu ko suka jikkata ba.
Artabun ya ɓarke ne a yankin Yankuzo da ke ƙaramar hukumar Tsafe lokacin da sojojin suka kutsa cikin wani maboyar da ake zargin tana da alaƙa da fitattun shugabannin ƙungiyoyin ‘yan bindiga da ke aiki a yankin.
Rahotannin tsaro sun bayyana cewa sojojin sun kai farmaki ne cikin yankin Ado Allero, wanda ake zargin yana daga cikin manyan sansanonin ‘yan bindiga.
Majiyoyin tsaro sun ce sojojin sun yi arangama da ‘yan bindigar ne da sanyin safiyar ranar Laraba, lamarin da ya haddasa doguwar musayar wuta da ta jefa tsoro a zukatan mazauna yankunan da ke kusa, inda aka riƙa jin ƙarar harbe-harbe masu ƙarfi na tsawon lokaci.
Ko da yake har yanzu ba a tantance yawan asarar rayuka ba, hukumomi sun tabbatar da cewa sojojin sun tsaya tsayin daka, sun mamaye yankin, kuma suna ci gaba da farautar waɗanda suka tsere.















Discussion about this post