Wasu ‘yan bindiga sun kai harin ramuwar gayya a ƙauyen Yankuzo da ke ƙaramar hukumar Tsafe a Jihar Zamfara, inda suka ƙone fadar Hakimin yankin, Alhaji Babangida Hamza, tare da sace kayayyaki bayan wani artabu da suka yi da sojoji na tsawon sa’o’i uku da aka kai maɓoyarsu a yankin.
Rahotanni sun ce maharan, ƙarƙashin jagorancin wani da ake kira Mai Rasha, sun mamaye ƙauyen a ranar Talata, suna harbe-harbe ba kakkautawa kafin su banka wa fadar Hakimin wuta.
“Sun shigo suna harbi kai tsaye suka nufi fadata suka ƙona ta,” in ji Hamza, wanda ya bayyana cewa yana garin Tsafe lokacin da harin ya faru.
Ya ƙara da cewa, an samu nasarar kwashe iyalansa zuwa wuri mai tsaro, amma har zuwa yammacin ranar Laraba ba a tantance yawan waɗanda suka mutu ko suka jikkata ba.
Mazauna yankin sun ce maharan sun shafe sa’o’i da dama a ƙauyen — har zuwa misalin ƙarfe 3:30 na rana — suna kwasar kayan abinci da sauran kayayyaki masu daraja daga shaguna daban-daban a wani shirinsu na wawashe dukiya.
Hakimin yankin ya bayyana cewa harin ramuwar gayya ne sakamakon samamen sojoji da suka kai sansanonin ‘yan ta’adda kusa da yankin a daren ranar.













Discussion about this post