ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bincike Ya Nuna Ƙungiyar Da Ta Zargi Gwamna Lawal Da Yi Wa ’Yan Bindiga Afuwa Ta Bogi Ce

by Sulaiman
6 months ago
Gwamna Lawal

An gano cewa zargin da ake yaɗawa cewa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi afuwa tare da sakin ‘yan bindiga da aka yanke wa hukunci ba shi da tushe kwata-kwata, bayan cikakken bincike da jaridar PremiumTimes ta gudanar kan batun da ya tayar da ƙura a kafafen yaɗa labarai.

 

A ranar 28 ga Nuwamban 2025, wata ƙungiya mai suna ‘Human Rights Watchdog in Africa’ (HRWA) ta fitar da wata sanarwa da aka ce daraktanta, Samson Adamu, ne ya sanya wa hannu, inda ta buƙaci Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya ayyana dokar ta-baci a Zamfara, bisa zargin cewa Gwamna Lawal ya yi afuwa tare da sakin ’yan bindiga 69 ta sirri, ƙarƙashin wani shiri da ta kira ‘Religious Amnesty.’

ADVERTISEMENT
  • Rashin Tsaro: Tinubu Ya Bada Sabbin Umarni Ga Shugabannin Sojoji
  • Gwamna Yusuf Ya Ziyarci Ƙananan Hukumomi 2 Kan Harin ‘Yan Bindiga A Yankunan 

Sai dai binciken da aka gudanar ya nuna cewa ba a samu asalin wannan sanarwa daga kowace sahihiyar majiya ba. Ƙokarin samun kungiyar HRWA da shugabanta Samson Adamu ya ci tura, domin babu wani ofishinta, lambar waya, shafin yanar gizo ko kuma rajistarta da aka samu a Hukumar Kula da Kamfanoni da Ƙungiyoyi ta Ƙasa. Haka nan, babu wani sahihin bayani ko sahihiyar shaidar da ke nuna wanzuwar ƙungiyar ko wannan mutum kafin ƙarshen Nuwamban 2025.

 

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Bincike ya kuma tabbatar da cewa abin da ya faru a zahiri shi ne Hukumar Zakka da Wakafi ta Jihar Zamfara ta taimaka wajen biyan basussukan fursunonin da aka yanke wa hukunci a shari’o’in farar hula, wanda hakan ya taimaka wajen sakin mutum 909 daga 2024 zuwa 2025. Wannan bayani ya fito ne daga bakin Sakataren Zartarwa na hukumar, Habib Muhammad Balarabe, a wani taron ƙarshen shekara da aka gudanar a Gusau.

 

A cewarsa, a 2024 kaɗai, an biya basussukan fursunoni 473, yayin da a 2025 aka kashe Naira miliyan 67.2 domin biyan basussukan mutum 436, wanda adadin gaba ɗaya ya kai 909 cikin shekaru biyu. Hukumar ta kuma bayar da tallafin jari ga mata 200 ƙanana ‘yan kasuwa da Naira dubu 50-50, tare da bai wa wasu mata 100 kayan fara sana’a bayan kammala horarwar kiwon kaji na makonni uku.

 

Jami’an hukumar Zakka sun bayyana cewa, ayyukansu na jinkai ba su taba shafar ‘yan bindiga da aka yanke wa hukunci kan laifukan ta’addanci ba. Wani jami’i da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, abin dariya ne ace gwamnan da ya sha bayyana a fili cewa ba ya sulhu da ‘yan bindiga shi ne zai koma ya sake su bayan an yanke musu hukunci.

 

Haka kuma, an tabbatar da cewa Gwamna Lawal bai taɓa sauya matsayarsa kan batun ‘yan bindiga ba. A ranar 29 ga Oktoban 2025, yayin da yake jawabi a gaban ɗaliban kwas ɗin tsaro a ‘National Institute for Security Studies’ da ke Abuja, gwamnan ya bayyana adawarsa ga yarjejeniyar sulhu da ‘yan bindiga da ake yi a wasu jihohin Arewa maso Yamma, yana mai cewa sulhu ba tare da ƙwace makamai ba hanya ce ta jinkirta tashin hankali.

 

Kakakin gwamnan, Suleman Bala Idris, ya musanta zargin baki ɗaya, yana mai cewa labarin ƙirƙirarre ne da wasu ‘yan siyasa da ke cikin matsin lamba suka tsara domin ɓata sunan gwamnatin Zamfara.

 

Ya jaddada cewa, babu wani lokaci da Gwamna Lawal ya yi afuwa ko ya saki kowane ɗan bindiga daga kurkuku.

 

Bayan kammala bincike mai zurfi, an tabbatar da cewa ƙungiyar HRWA da shugaban nata kamar fatalwa ne, kuma zargin da aka yi cewa Gwamna Lawal ya saki ‘yan bindiga ƙarya ne tsagwaron gaske.

Gwamna Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
2027: Ba Mu Da Hujjar Juyawa Gwamna Uba Sani Da Tinubu Baya — Tsohon Gwamnan Kaduna

2027: Ba Mu Da Hujjar Juyawa Gwamna Uba Sani Da Tinubu Baya — Tsohon Gwamnan Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.