A baya-bayan nan, ‘yan majalisar dokokin kasar Faransa sun amince da daftarin dokar saukaka mayar da kayan tarihi na gargajiya, da aka wawashe yayin mulkin mallaka ga kasashensu na asali.
Game da hakan, wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta gudanar, ya shaida yadda kaso 67.6 bisa dari na masu bayyana mahangarsu, suka amince cewa wannan kudurin doka na wakiltar matakin farko na shari’a da Faransa ta dauka, da nufin fuskanta, da gyara kura-kuran da ta tafka a tarihin mulkin mallaka da ta aikata.
Sakamakon binciken ya nuna kaso 90.8 bisa dari na wadanda suka bayyana ra’ayoyinsu, sun gamsu da matakin ‘yan majalisun dokokin na Faransa.
A daya bangaren kuma, kaso 85.4 bisa dari na ganin hakan ya karyata matsayar wasu daga masu fada a ji cikin ‘yan mulkin mallaka, dake ganin zai iya yiwuwa a halasta irin wadannan kayayyaki da aka wawashe, kana hakan zai sa sauran kasashen da suka aikata wannan ta’asa su sake nazari, dangane da manufofinsu game da wawashe kayan tarihin kasashen da suka yiwa mulkin mallaka.Kafar CGTN ta gabatar da binciken jin ra’ayin jama’ar ne ta harsunan Turancin Ingilishi, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci da harshen kasar Rasha, inda masu bayyana ra’ayoyi 4,127 na sassan kasa da kasa suka gabatar da mahangarsu ta dandalin intanet cikin sa’ao’i 24. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post