Shugaba Bola Tinubu, ya ce kyawawan manufofi da abubuwan da tsohon Shugaba Muhammadu Buhari ya bari za su ci gaba da zaburar da ’yan Nijeriya na tsawon shekaru masu zuwa.
Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a Abuja yayin taron addu’ar cika shekara ɗaya da rasuwar Buhari.
Mataimakinsa, Kashim Shettima ne, ya wakilce shi a wajen taron.
Shugaban ya bayyana Buhari a matsayin shugaba mai kishin ƙasa wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa Nijeriya hidima da kuma taimakawa wajen ci gaban ƙasar.
Ya ce za a ci gaba da tunawa da Buhari saboda gaskiya, ladabi da jajircewarsa wajen yi wa jama’a hidima.
Tinubu ya ce har yanzu ’yan Nijeriya da dama na mutunta Buhari duk da cewa ya bar mulki, sannan ya ƙarfafa wa jama’a gwiwa su ci gaba da riƙe ƙa’idoji wajen gudanar da rayuwa.
Ya ce Nijeriya ba za ta manta da Buhari ba saboda irin rayuwar da ya yi da kuma gudummawar da ya bayar wajen ci gaban ƙasar.
Tinubu ya tuna da dangantakarsa ta siyasa da Buhari, inda ya ce sun yi aiki tare bisa manufa ɗaya ta gina Nijeriya mai zaman lafiya, haɗin kai da wadata.
Ya ƙara da cewa Buhari ya yi wa ƙasar hidima da ƙarfinsa da sadaukarwa.
A cewar Tinubu, Buhari na daga cikin ’yan Nijeriya da suka jagoranci ƙasar a matsayin shugaban soji sannan kuma suka zama shugaban ƙasa ta hanyar zaɓen dimokuraɗiyya.
Ya ce tasirin Buhari ya ginu ne a kan gaskiya, ɗabi’a ta gari da hidimar jama’a, ba wai neman yabo ba.
Shugaban ya kuma miƙa ta’aziyya ga iyalan Buhari tare da tabbatar musu cewa gwamnati za ta ci gaba da kasancewa tare da su.
Ya ce ya kamata ’yan Nijeriya su yi riƙo da halayen da Buhari ya yi fice da su, kamar gaskiya da sauƙin kai.
Tsohon shugaban ƙasa na mulkin soji, Janar Yakubu Gowon, shi ma ya karrama Buhari, inda ya bayyana shi a matsayin jarumin soja da ya yi aiki don tabbatar da haɗin kan Nijeriya.
Gowon ya ce nasarar Buhari a siyasa ta ƙara ƙarfi ne bayan ya yi haɗin gwiwa da Tinubu, wanda ya taimaka masa wajen lashe zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2015.













