Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da sabbin ƙa’idoji da za su jagoranci shirin dawo da tubabbun ’yan ta’adda cikin al’umma.
Gwamnatin ta ce shirin zai taimaka wajen gyara rayuwar tsoffin ’yan ta’addan tare da taimaka musu su koma rayuwar yau da kullum, amma waɗanda ake zargi da aikata manyan laifuka za su fuskanci hukuncin doka.
Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC) ta bayyana cewa sabbin ƙa’idojin za su inganta gaskiya, haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da kuma kare haƙƙin ɗan Adam.
Shugaban NCTC, Adamu Laka, ya ce amfani da ƙarfin soji kaɗai ba zai kawo ƙarshen rashin tsaro ba.
Ya bayyana cewa shirin na daga cikin matakan da Nijeriya ke ɗauka don samar da zaman lafiya.
Majalisar Ɗinkin Duniya ta yaba da tsarin Nijeriya, inda ta ce samun zaman lafiya yana buƙatar haɗin kan al’umma, hukumomin gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki.













