Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, ya ce an samu tsaro a Ƙaramar Hukumar Jibia, lamarin da ya sa manoma suka koma gonakinsu domin ci gaba da noma.
Gwamnan ya bayyana haka ne yayin ƙaddamar da gidaje 152 da Hukumar UNDP tare da gwamnatin jihar suka gina wa mutanen da hare-haren ‘yan bindiga suka raba da muhallansu a Jibia.
Radda ya ce fiye da shekara guda kenan ba a samu wani harin ‘yan bindiga ko sace mutane a ƙaramar hukumar, abin da ya nuna cewa an samu zaman lafiya a yankin.
Ya ƙara da cewa kasuwannin da aka rufe a baya sun koma aiki, yara sun koma makaranta, sannan farashin kayan abinci ya ragu.
Gwamnan ya kuma buƙaci al’umma su kasance masu taimakawa wajen tabbatar da tsaro, yana mai cewa tsaro nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa, ba gwamnati kaɗai ba.
“Tsaro ba aikin gwamnati kawai ba ne. Ana iya taimakawa wajen samar da tsaro a gida, kasuwa, masallaci da sauran wuraren taruwar jama’a,” in ji shi.
Haka kuma, ya yi kira ga ‘yan bindigar da har yanzu ke cikin daji da su ajiye makamansu su rungumi zaman lafiya.
Ya ce har yanzu gwamnati a shirye take ta karɓi duk wanda ya tuba ya kuma ajiye makamansa domin ya dawo ya zauna cikin al’umma tare da iyalansa cikin kwanciyar hankali.














Discussion about this post