Ayyukan hukumar leken asiri na kasa sun jima da kasancewa muhimmin jigo na fadada ayyukan soji.
Manufar masu tsattsauran ra’ayi na Japan na ingiza ayyukan hukumar leken asiri ta kasar na da matukar hadurra, wadanda za su iya mayar da al’ummun Japan kan turbar fuskantar nuna karfin tuwo ga sassan ketare. Wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, ya nuna yadda kaso 84.8 bisa dari na masu bayyana mahangarsu suka amince, cewa masu tsattsauran ra’ayi na Japan sun yi yunkurin karfafa ayyukan leken asiri, a matsayin karin mataki mai hadari don cimma bukatar fadada karfin soji, matakin dake bukatar matukar lura daga al’ummun kasa da kasa.
Bisa dokar da ‘yan majalisar dokokin kasar Japan suka kafa a jiya Laraba, tsarin aikin leken asiri na kasar zai mayar da hankali ga ayyukan majalisar tattara bayanan sirri ta kasa, inda hukumar leken asirin kasar za ta zama wadda za ta rika gudanar da ayyukan.
Kuma bayan kafuwarta, za ta dinke sassan hukumomin dake gudanar da ayyuka masu nasaba da hakan wuri guda. Hakan na nufin kawar da tsarin rukunoni daban daban masu ayyukan leken asiri da Japan ta kawar bayan kammala yakin duniya na biyu, tare da dunkule karfin tattara bayanan sirri a karkashin ikon firaministan kasar.
Sakamakon binciken na CGTN, kaso 86.5 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyi na ganin wannan babban sauyi ne ga tsarin ayyukan tattara bayanan sirri na Japan bayan yaki, yayin da kaso 77.7 bisa dari suka amince cewa hakan na iya kaiwa ga amfani da karfi ba bisa ka’ida ba, kana mataki ne na watsi da nazari, da daidaito da sanya ido. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post