ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ya Nuna Yadda ’Yan Peru Ke Fatan Ganin An Samar Da Salon Kasa Na Hadin Gwiwa

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Peru

Kasar Peru makwafciyar kasar Sin ce ta bangaren tekun Pacifik, kuma fadadar kusancin sassan biyu ta fuskar tattalin arziki, da hadin gwiwar cinikayya, da musayar al’adu, na ci gaba da matso da kasashen biyu kusa da juna, a matsayin kawaye kuma makwafta a yankin tekun Pacifik. 

 

Yayin ziyarar shugaban kasar Sin Xi Jinping kasar Peru, a karon farko, kafar watsa labarai ta CGTN, karkashin cibiyar tattauna harkokin kasa da kasa a sabon zamani, da cibiyar zurfafa bincike game da harkokin kasa ta Peru, sun kaddamar da wani binciken jin ra’ayin jama’a, game da karbuwar kasar Sin tsakanin al’ummun kasar Peru a shekarar 2024 inda ’yan kasar Peru 1,111 suka bayyana ra’ayoyinsu.

ADVERTISEMENT
  • Sin Ta Harba Kumbon Tianzhou-8 Na Dakon Kayayyaki Zuwa Tashar Binciken Samaniya Ta Tiangong
  • Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

Sakamakon binciken ya nuna yadda masu bayyana ra’ayoyin suka yi amanna da kawancen gargajiya tsakanin Sin da Peru, da nasarar hadin gwiwarsu, tare da fatan ganin an gina “Salon kasar Peru” na inganta alakar Sin da kasashen Latin Amurka, da bunkasa hadin gwiwa bisa matsayin koli, tsakanin kasashe masu tasowa da masu saurin samun ci gaba.

 

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

A matsayin Sin na kasa mai tasowa mafi girma a duniya, nasarorin da ta cimma, da mahangarta ta zamanantarwa, sun samar da wata gogewa, da tarin damammaki ga kasashe masu tasowa da masu saurin samun ci gaba.

 

Kazalika, sakamakon binciken ya nuna yadda masu bayyana ra’ayoyin suka gamsu da nasarorin da kasar Sin ta samu, ta fuskar ci gaba mai inganci da bude kofa bisa matsayin koli.

 

Cikin masu bayyana ra’ayoyin, kaso 97.2% sun yaba da saurin bunkasar tattalin arzikin kasar Sin. Kana kaso 94.8% sun amince cewa tattalin arzikin kasar zai ci gaba da bunkasa. Har ila yau, kaso 89.9% sun gamsu da muhimmancin gudummawar kasar Sin ta fuskar ingiza daidaito a tsarin rarraba hajojin masana’antu tsakanin sassan duniya.

 

A daya hannun kuma, kaso 85.7% na ganin Sin na da babbar kasuwa wadda ke bude, kuma mai karbar takara ta adalci. Akwai kuma kaso 96.6% da suka yabawa kasar Sin, bisa muhimmiyar gudummawa da ta bayar wajen farfado da tattalin arzikin duniya. (Saminu Alhassan)

Peru
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
Peru
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
Daga Birnin Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
Daga Birnin Sin

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
Next Post
Shahararrun Mutanen Da Suka Halarci Bikin Auren ‘Yar Kwankwaso

Shahararrun Mutanen Da Suka Halarci Bikin Auren ‘Yar Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.