Ƙungiyar Boko Haram ta amince da wani tsari da aka gabatar domin yiwuwar sakin mata da yara 50 da ta sace daga Ngoshe a Jihar Borno, kuma aka tsare tsawon makonni ana tattaunawa da shiga tsakani.
Wata ƙungiya mai suna Borno South Youth Alliance (BOSYA) ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook da aka tabbatar da sahihancinsa a ranar Talata.
BOSYA ta ce an samu wannan ci gaba ne bayan “tattaunawa masu zurfi da taka-tsantsan” da aka yi da ɓangaren ƙungiyar da ake kira Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal-Jihad (JAS).
“Ƙungiyar BOSYA na sanar da ‘yan Nijeriya da al’ummar Kudancin Borno cewa, bayan dogon lokaci na tattaunawa da shiga tsakani cikin taka-tsantsan, JAS (Boko Haram) ta amince da wani tsari da aka gabatar domin yiwuwar sakin mata da yara 50,” in ji ƙungiyar.
BOSYA ta kuma yaba wa Rundunar Sojin Nijeriya bisa rawar da take takawa wajen ƙoƙarin tabbatar da ‘yantar da waɗanda aka sace















Discussion about this post