Gwamnatin Jihar Sokoto ta tabbatar da mutuwar yara 33 sakamakon barkewar cutar sankarau a wasu sassan jihar.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Faruk Abubakar, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin wani taron wayar da kai da hakimai da kungiyoyin SARMAAN MNTE.
Hukumar Bunƙasa Kiwon Lafiya a Matakin Farko ta jihar ce ta shirya taron tare da haɗin gwiwar ƙungiyar Sightsavers da gidauniyar Chigari.
A cewar kwamishinan, an samu rahoton mutane 256 da ake zargin sun kamu da cutar a ƙananan hukumomi takwas na jihar tun bayan sake ɓullar cutar kusan wata guda da ya gabata.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mazauna ƙauyen Kurawa da ke ƙaramar hukumar Sabon Birni su suka fara sanar da zargin ɓarkewar cutar, wadda suka ce ta fi shafar yara da matasa.
Majiyoyi daga cibiyar lafiya ta ƙauyen sun kuma shaida cewa lamarin ya ƙara muni, inda ake samun mace-mace tsakanin mutum biyu zuwa uku a kullum, galibi tsakanin masu shekaru biyu zuwa 20.















Discussion about this post